Shugaban Jam’iyyar PRP na ƙasa, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ya ce cire gwamnatin APC ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga mulki a zaɓen shekarar 2027 abu ne mai yiwuwa.
Baba-Ahmed, wanda ya bayyana haka a shirin ‘Sunday Politics’ na gidan talabijin na Channels, ya ce gwamnatin ta sauƙaƙa yiwuwar shan kayenta saboda mawuyacin halin rayuwa da ta jefa ‘yan Nijeriya ciki.
Tsohon mai bai wa shugaban ƙasa shawara ya kuma ce jam’iyyarsa a shirye take domin zaɓen 2027, amma za ta yi aiki tare da wasu jam’iyyun adawa domin tabbatar da kayar da APC da Tinubu a zaɓe.
A cewarsa, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, da jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ba su samu shiga PRP ba saboda buƙatar da suka bayar ta a ba su tikitin takarar shugaban ƙasa kai tsaye, amma har yanzu suna da matsayin abokan siyasa na kusa.
Ya ce za a iya tantance ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ne kawai ta hanyar gudanar da manyan tarukan jam’iyya ko babban taron ƙasa, ba ta wata hanya daban ba.















Discussion about this post