Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince gwamnatin Jihar Katsina ta ɗauki ma’aikatan gandun daji mutum 1,000 waɗanda za su tsare dazuzukan da ke fama da matsalolin tsaron a Jihar baƙi ɗaya
Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya bayyana haka a jin kaɗan bayan kammala wani taron gaggawa da yi da Malamai a Katsina
Gwamnan Jihar Katsina ya ce shugaban ƙasa Bola Tinubu da kansa ya amince a ɗauki ma’aikatan gandun daji guda dubu ɗaya, domin tsare dazuzuka a Jihar Katsina.
“Ina miƙa godiya ta bisa wannan al’amari na amincewar shugaban ƙasa da ya amsa rokon mu na ɗaukar ma’aikatan gandun daji 1,000 wanda za a ɗauki matasa maza da mata wanda kuma za su yi aiki tare da hukumomin tsaro” inji shi
Gwamnan wanda ya nuna irin ƙoƙarin da ake yi na ganin an kawo ƙarshen matsalolin tsaro ta hanyar haɗa kai da Malaman Addini a matsayin wani bangare da za a iya samun cigaba da zaman lafiya tare da lalubo hanyar magance matsalolin tsaro.
Dikko Raɗɗa wanda ya ce tattaunawa da malamai ya zama wajibi domin ta haka ne za su san girman matsalar tsaro tare da neman hanyar warware matsalolin ta fuskoki da dama.
Ya ce dalilin wannan zama da malaman addini shi ne domin su ji kai tsaye daga wajen Malaman sannan su fahimci yanayin halin tsaro da ake ciki daga ƙarshe a nemi shawarar su wajan magance ta.
Ya ƙara da cewa girman wannan matsala ta kai inda ba za a iya barin jami’an tsaro da ita ba su kaɗai, shigowar al’umma musamman malamai zai zama hanyar samun zaman lafiya
Gwamna Raɗɗa ya bayyana cewa bincike ya tabbatar da cewa akwai masu taimakon ƴan bindiga a cikin al’umma, ta hanyar bada bayanan sirri da kuma sayar da shanun da aka barayin dajin suka sato
Kazalika gwamna Raɗɗa ya yabawa gwamantin tarayya ƙarƙashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu saboda taimakon da ta yi na ƙara turo jami’an tsaro a Jihar Katsina
“Yanzu mun ƙara samun jami’an tsaro da dama da suka haɗa da sojoji da ƴan sanda da jami’an hukumar farin kaya ta DSS wanda hakan ke ƙara ƙarfafa mana gwiwa cewa dole mu nuna godiya ƙwarai da gaske” inji shi
Daga ƙarshe ya yi kira ga al’ummar Jihar Katsina da su kasance masu lura da abubuwan da ke zuwa suna dawowa domin ta haka ne za taimakawa gwamnati wajen dawowa da zaman lafiya.















Discussion about this post