Fafatawar siyasa domin samun kuri’un masu zaɓe kusan miliyan 5.9 na Jihar Kano a zaɓen 2027 ta ƙara ɗaukar zafi, yayin da manyan jam’iyyu da ‘yan siyasa ke ƙara ƙoƙarin samun karɓuwa a jihar.
Jihar Kano na da muhimmiyar rawar takawa a zaɓen shugaban ƙasa saboda yawan masu rajista da kuma tasirin siyasar jihar a yankin Arewa. A zaɓen shugaban ƙasa na 2023, adadin masu rajistar zaɓe a jihar ya kai 5,921,370.
A yayin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke neman wa’adin mulki na biyu a ƙarƙashin APC, ‘yan adawa irin su Atiku Abubakar da sauran manyan ‘yan siyasa na ƙoƙarin haɗa ƙarfi domin ƙalubalantar jam’iyyar mai mulki a 2027.
Kano ta kasance muhimmiyar jiha ga siyasar tsohon gwamna Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya samu gagarumar nasara a jihar a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, lamarin da ya ƙara nuna muhimmancin tasirin masu zaɓe na jihar a fafatawar matakin ƙasa.
Yayin da ake tunkarar 2027, fafatawar za ta fi karkata ne kan wanda zai iya haɗa ƙungiyoyin siyasa, da shugabannin al’umma da masu zaɓe a matakin ƙasa da ƙananan hukumomi, domin samun rinjaye a jihar da ke da ɗaya daga cikin manyan wuraren cunkoson ƙuri’u a Nijeriya.














