’Yan bindiga sun kai wa manoma hari a ƙauyen Tse Uyoo da ke Ƙaramar Hukumar Ukum a Jihar Benue, inda suka kashe wani manomi sannan suka yanke wa hannu.
Harin ya faru ne yayin da manoma ke girbin lemun tsami.
- Sin Ba Za Ta Amince Da Amfani Da Karfin Tuwo Yayin Da Ake Daidaita Huldar Kasa Da Kasa Ba
- Hadin Gwiwa Tsakanin Canada Da Sin Zai Iya Kai Su Ga Samun Ci Gaba Cikin Zaman Lafiya Da Wadata
Mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun riƙa kai hare-hare kan gonaki a cikin ƙaramar hukumar Ukum, da Logo, Guma, Otukpo, Agatu, da Kwande a ‘yan makonnin nan.
A wasu lokuta, su kan lalata amfanin gona, sun kuma ƙone babura, yayin da manoma sun gudu daga gonakinsu.
An kuma samu rahoton cewa sun kashe kashe wani manomi a ƙaramar hukumar Otukpo a ƙarshen mako, yayin da ’yan bindiga suka kai hari a yankin Adoka makon da ya gabata, suka lalata amfanin gonakin da aka girbe sannan suka tilasta mutane tserewa.
Hare-hare a ƙauyen Adogo sun shafar manoma a ƙaramar hukumar Ukum da Logo.
Wani mazaunin yankin Ogobia, Alfred Edoga, ya yi kira ga gwamnati da ta kawowa manoma ɗauki.
’Yansanda ba su fitar da wata sanarwa game da waɗannan hare-hare ba.















Discussion about this post