’Yansanda a ƙasar Mali sun kama wani boka da ake zargi da karɓar kusan euro €33,500 bayan ya yi alƙawarin cewa ƙasar Mali za ta lashe gasar AFCON ta 2025.
An kama bokan, mai suna Sinayogo, a birnin Bamako bayan Mali ta sha kashi da ci 1–0 a hannun Senegal a wasan daf da na kusa da na ƙarshe.
- Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Bunkasa Sayayya Da Bude Kofa A Shekarar 2026
- Shettima Ya Ce Zuba Jari A Ɓangaren Ilimi Ba Caca Ba Ce
Rahotanni sun ce ya karɓi sama da CFA franc miliyan 22 daga magoya baya da suka yi imanin cewa zai iya amfani da sihiri ko tsafi wajen tabbatar da nasarar tawagar ƙasar.
Bayan rashin nasarar Mali a gasar, wasu fusatattun magoya baya sun kai hari gidansa, sai dai ’yansanda sun shiga tsakani suka kwantar da tarzomar.
Hukumomi sun ce an kama bokan ne bisa zargin aikata damfara, domin yin iƙirari inda suka ce hakan ya saɓa wa doka a Mali.















Discussion about this post