Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, ya mika fom ɗinsa na takarar gwamna ga Kwamitin Gudanarwa na ƙasa na jam’iyyar APC a Abuja, a matsayin ɗan takarar jam’iyyar shi kaɗai a zaɓen 2027.
A cewar wata sanarwa da aka fitar ranar Juma’a, gwamnan ya isa tare da manyan jiga-jigan siyasa da suka haɗa da Malam Ibrahim Shekarau, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibrin, da Kawu Sumaila da wasu ’yan Majalisar Wakilai da sauran manyan baƙi.
Da yake zantawa da manema labarai bayan mika fom ɗin a Treasure Suites, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa ayyana shi a karo na biyu wani sabon kira ne na ci gaba da yi wa al’ummar Kano hidima tare da ƙara himma wajen bunƙasa jihar.
Ya ce gwamnatinsa za ta faɗaɗa ayyukan raya birane, ciki har da gina hanyoyi, da magudanan ruwa da sabunta kasuwanni, tare da mai da hankali sosai kan ci gaban karkara ta hanyar samar da hanyoyin ƙauyuka, da ruwa, da cibiyoyin lafiya da makarantu.
Gwamnan ya kuma yi alƙawarin ƙara tallafa wa noma da shirye-shiryen bunƙasa matasa, yana mai cewa samar da ayyukan yi, da inganta ilimi da kiwon lafiya, da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai za su ci gaba da kasancewa manyan manufofin gwamnatinsa.















Discussion about this post