Rahotanni daga kafofin yada labaran Iran sun bayyana cewa sojojin Iran sun harba makamai masu linzami kan wani jirgin ruwan yakin Amurka domin hana shi shiga Mashigar Hormuz.
Har yanzu dai babu wata majiya mai zaman kanta da ta tabbatar da ikirarin, hakazalika Amurka ma ba ta ce komai ba.
Rahotannin harin na zuwa ne bayan da Iraniyawa suka ce za su kai hari kan dakarun Amurka idan har suka aiwatar da shirin Shugaba Trump na yi wa jiragen ruwan kasuwanci wadanda suka makale rakiya ta Mashigar.
Iran din ta ce wajibi ne a hada kai da ita kafin wani jirgi ya wuce lafiya.
Rundunar sojin Amurka ta ce za ta aike da jiragen ruwan yaki da kuma jiragen sama, domin su bai wa jirage shawarar hanyoyin da za su bi su wuce, kuma su samar da garkuwa ga duk wani hari da Iran za ta kai.
Daruruwan jiragen ruwan kasuwanci, da akalla ma’aikata dubu ashirin ne suka makale a yankin tun bayan soma yakin Amurka da Iran watanni biyu da suka gabata.















Discussion about this post