Hukumar samar da ruwa da inganta tsaftar muhalli a yankunan karkara ta Jihar Katsina (RUWASSA) ta ce tana kwazo domin tabbatar da aiwatar da ayyukan samar da ruwa a fadin yankunan kananan hukumomi jihar.
Aikin da take yi yanzu haka ya kunshi kananan hukumomin Batagarawa, Baure, Daura, Funtua, Kafur da Katsina da ake aiwatarwa karkashin shirin SURWASH, wanda gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar Bankin Duniya suke daukar nauyi.
- Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Matafiya 20 A Jihar Neja
- Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara
Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur wanda ya yi magana a lokacin ziyarar duba wasu wurare a Katsina da Batagarawa. Ya ce hukumar na da kudirin tabbatar da cewa an aiwatar da aikin daidai da yadda aka tsara, domin amfanar al’ummomin yadda ya kamata.
Ya bayyana gamsuwa kan ginin wasu wurare, inda ya hori ‘yan kwangilar su tabbatar da cewa dukkanin wasu korafe-korafe da tsare-tsare da suka shafi aikin an shawo kansu kafin a hannata ayyukan ga hukumar.
Daga cikin wuraren da aka duba a lokacin ziyarar sun hada da famfunan hannu da famfuna masu amfani da hasken rana a Kambarawa layin Kawu, Kwado da Bayan Gidan Taki a Katsina da kuma Borar Gunduwa ‘A’ and ‘B’ a yankin karamar hukumar Batagarawa.
A lokacin ziyarar, Alhaji Abubakar Abukur ya tattauna da wasu al’ummomin da za su amfana da ayyukan samar da ruwan da jami’an kwamitocin samar da ruwa da inganta tsare-tsaren ayyukan, gyara da kula da wuraren.
Haka nan kuma, a halin da ake ciki gwamnatin Jihar Katsina ta gina karin famfuna masu amfani da hasken rana a sansanin rundunar sojojin saman Nijeriya da ke Katsina.
Wannan wani Bangare ne na shiri na musamman da gwamnatin Dikko Radda ke gudanarwa da bunkasa samar da ruwan sha.
Da yake gabatar da jawabi a lokacin hannanta wurare samar da ruwa a sansanin, shugaban hukumar RUWASSA, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur ya ce shirin na da nufin rage karancin ruwa a cikin sansanin.
Ya ce aikin ya kunshi hada famfunan da wurin tara ruwa da ke sansanin da kuma sake tsarin sassa daban-daban don al’ummar sansanin su samu damar amfana da wuraren yadda ya kamata.
Da yake mayar da jawabi, mukkaddashin kwamandan sansanin, Wing Commander N.C Okorie ya bayyana godiya ga Gwamna Radda bisa aiwatar da aikin samar da ruwa a sansanin. Ya yi alkawarin cewa al’ummomin da za su amfana za su kula da wuraren samar da ruwa yadda ya kamata.















Discussion about this post