ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar and Sulaiman
3 months ago
ruwassa

Hukumar samar da ruwa da inganta tsaftar muhalli a yankunan karkara ta Jihar Katsina (RUWASSA) ta ce tana kwazo domin tabbatar da aiwatar da ayyukan samar da ruwa a fadin yankunan kananan hukumomi jihar. 

Aikin da take yi yanzu haka ya kunshi kananan hukumomin Batagarawa, Baure, Daura, Funtua, Kafur da Katsina da ake aiwatarwa karkashin shirin SURWASH, wanda gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar Bankin Duniya suke daukar nauyi.

  • Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Matafiya 20 A Jihar Neja
  • Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur wanda ya yi magana a lokacin ziyarar duba wasu wurare a Katsina da Batagarawa. Ya ce hukumar na da kudirin tabbatar da cewa an aiwatar da aikin daidai da yadda aka tsara, domin amfanar al’ummomin yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana gamsuwa kan ginin wasu wurare, inda ya hori ‘yan kwangilar su tabbatar da cewa dukkanin wasu korafe-korafe da tsare-tsare da suka shafi aikin an shawo kansu kafin a hannata ayyukan ga hukumar.

Daga cikin wuraren da aka duba a lokacin ziyarar sun hada da famfunan hannu da famfuna masu amfani da hasken rana a Kambarawa layin Kawu, Kwado da Bayan Gidan Taki a Katsina da kuma Borar Gunduwa ‘A’ and ‘B’ a yankin karamar hukumar Batagarawa.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A lokacin ziyarar, Alhaji Abubakar Abukur ya tattauna da wasu al’ummomin da za su amfana da ayyukan samar da ruwan da jami’an kwamitocin samar da ruwa da inganta tsare-tsaren ayyukan, gyara da kula da wuraren.

Haka nan kuma, a halin da ake ciki gwamnatin Jihar Katsina ta gina karin famfuna masu amfani da hasken rana a sansanin rundunar sojojin saman Nijeriya da ke Katsina.

Wannan wani Bangare ne na shiri na musamman da gwamnatin Dikko Radda ke gudanarwa da bunkasa samar da ruwan sha.

Da yake gabatar da jawabi a lokacin hannanta wurare samar da ruwa a sansanin, shugaban hukumar RUWASSA, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur ya ce shirin na da nufin rage karancin ruwa a cikin sansanin.

Ya ce aikin ya kunshi hada famfunan da wurin tara ruwa da ke sansanin da kuma sake tsarin sassa daban-daban don al’ummar sansanin su samu damar amfana da wuraren yadda ya kamata.

Da yake mayar da jawabi, mukkaddashin kwamandan sansanin, Wing Commander N.C Okorie ya bayyana godiya ga Gwamna Radda bisa aiwatar da aikin samar da ruwa a sansanin. Ya yi alkawarin cewa al’ummomin da za su amfana za su kula da wuraren samar da ruwa yadda ya kamata.

 

ruwassa
Sagir Abubakar
+ posts Bio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Barayin Shanu Sun Kashe DPO A Karamar Hukumar Rimi Ta Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Radda Ya Rantsar Da Sabon Mai Shari’a, Khadi Mustapha Salisu
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
ruwassa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.