ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar and Sulaiman
4 months ago
ruwassa

Hukumar samar da ruwa da inganta tsaftar muhalli a yankunan karkara ta Jihar Katsina (RUWASSA) ta ce tana kwazo domin tabbatar da aiwatar da ayyukan samar da ruwa a fadin yankunan kananan hukumomi jihar. 

Aikin da take yi yanzu haka ya kunshi kananan hukumomin Batagarawa, Baure, Daura, Funtua, Kafur da Katsina da ake aiwatarwa karkashin shirin SURWASH, wanda gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar Bankin Duniya suke daukar nauyi.

  • Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Matafiya 20 A Jihar Neja
  • Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur wanda ya yi magana a lokacin ziyarar duba wasu wurare a Katsina da Batagarawa. Ya ce hukumar na da kudirin tabbatar da cewa an aiwatar da aikin daidai da yadda aka tsara, domin amfanar al’ummomin yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana gamsuwa kan ginin wasu wurare, inda ya hori ‘yan kwangilar su tabbatar da cewa dukkanin wasu korafe-korafe da tsare-tsare da suka shafi aikin an shawo kansu kafin a hannata ayyukan ga hukumar.

Daga cikin wuraren da aka duba a lokacin ziyarar sun hada da famfunan hannu da famfuna masu amfani da hasken rana a Kambarawa layin Kawu, Kwado da Bayan Gidan Taki a Katsina da kuma Borar Gunduwa ‘A’ and ‘B’ a yankin karamar hukumar Batagarawa.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

A lokacin ziyarar, Alhaji Abubakar Abukur ya tattauna da wasu al’ummomin da za su amfana da ayyukan samar da ruwan da jami’an kwamitocin samar da ruwa da inganta tsare-tsaren ayyukan, gyara da kula da wuraren.

Haka nan kuma, a halin da ake ciki gwamnatin Jihar Katsina ta gina karin famfuna masu amfani da hasken rana a sansanin rundunar sojojin saman Nijeriya da ke Katsina.

Wannan wani Bangare ne na shiri na musamman da gwamnatin Dikko Radda ke gudanarwa da bunkasa samar da ruwan sha.

Da yake gabatar da jawabi a lokacin hannanta wurare samar da ruwa a sansanin, shugaban hukumar RUWASSA, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur ya ce shirin na da nufin rage karancin ruwa a cikin sansanin.

Ya ce aikin ya kunshi hada famfunan da wurin tara ruwa da ke sansanin da kuma sake tsarin sassa daban-daban don al’ummar sansanin su samu damar amfana da wuraren yadda ya kamata.

Da yake mayar da jawabi, mukkaddashin kwamandan sansanin, Wing Commander N.C Okorie ya bayyana godiya ga Gwamna Radda bisa aiwatar da aikin samar da ruwa a sansanin. Ya yi alkawarin cewa al’ummomin da za su amfana za su kula da wuraren samar da ruwa yadda ya kamata.

 

ruwassa
Sagir Abubakar
+ posts Bio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Barayin Shanu Sun Kashe DPO A Karamar Hukumar Rimi Ta Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Radda Ya Rantsar Da Sabon Mai Shari’a, Khadi Mustapha Salisu
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
ruwassa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.