ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar and Sulaiman
5 months ago
ruwassa

Hukumar samar da ruwa da inganta tsaftar muhalli a yankunan karkara ta Jihar Katsina (RUWASSA) ta ce tana kwazo domin tabbatar da aiwatar da ayyukan samar da ruwa a fadin yankunan kananan hukumomi jihar. 

Aikin da take yi yanzu haka ya kunshi kananan hukumomin Batagarawa, Baure, Daura, Funtua, Kafur da Katsina da ake aiwatarwa karkashin shirin SURWASH, wanda gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar Bankin Duniya suke daukar nauyi.

  • Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Matafiya 20 A Jihar Neja
  • Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur wanda ya yi magana a lokacin ziyarar duba wasu wurare a Katsina da Batagarawa. Ya ce hukumar na da kudirin tabbatar da cewa an aiwatar da aikin daidai da yadda aka tsara, domin amfanar al’ummomin yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana gamsuwa kan ginin wasu wurare, inda ya hori ‘yan kwangilar su tabbatar da cewa dukkanin wasu korafe-korafe da tsare-tsare da suka shafi aikin an shawo kansu kafin a hannata ayyukan ga hukumar.

Daga cikin wuraren da aka duba a lokacin ziyarar sun hada da famfunan hannu da famfuna masu amfani da hasken rana a Kambarawa layin Kawu, Kwado da Bayan Gidan Taki a Katsina da kuma Borar Gunduwa ‘A’ and ‘B’ a yankin karamar hukumar Batagarawa.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

A lokacin ziyarar, Alhaji Abubakar Abukur ya tattauna da wasu al’ummomin da za su amfana da ayyukan samar da ruwan da jami’an kwamitocin samar da ruwa da inganta tsare-tsaren ayyukan, gyara da kula da wuraren.

Haka nan kuma, a halin da ake ciki gwamnatin Jihar Katsina ta gina karin famfuna masu amfani da hasken rana a sansanin rundunar sojojin saman Nijeriya da ke Katsina.

Wannan wani Bangare ne na shiri na musamman da gwamnatin Dikko Radda ke gudanarwa da bunkasa samar da ruwan sha.

Da yake gabatar da jawabi a lokacin hannanta wurare samar da ruwa a sansanin, shugaban hukumar RUWASSA, Alhaji Abubakar Suleiman Abukur ya ce shirin na da nufin rage karancin ruwa a cikin sansanin.

Ya ce aikin ya kunshi hada famfunan da wurin tara ruwa da ke sansanin da kuma sake tsarin sassa daban-daban don al’ummar sansanin su samu damar amfana da wuraren yadda ya kamata.

Da yake mayar da jawabi, mukkaddashin kwamandan sansanin, Wing Commander N.C Okorie ya bayyana godiya ga Gwamna Radda bisa aiwatar da aikin samar da ruwa a sansanin. Ya yi alkawarin cewa al’ummomin da za su amfana za su kula da wuraren samar da ruwa yadda ya kamata.

 

ruwassa
Sagir Abubakar
+ posts Bio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Barayin Shanu Sun Kashe DPO A Karamar Hukumar Rimi Ta Jihar Katsina
ruwassa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Jam’iyyar NNPP Ta Yi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.