Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da yin garambawul ga Shirin Yi wa Ƙasa Hidima na Matasa (NYSC).
Ministan Raya Matasa, Ayodele Olawande, ne ya bayyana hakan.
Da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa bayan taron majalisar da aka gudanar a ranar Litinin, ministan ya ce garambawul ɗin zai haɗa da cikakken nazari da sake fasalin shirin na NYSC.
An kafa shirin NYSC ne a shekarar 1973 domin inganta haɗin kan ƙasa bayan yaƙin basasar Nijeriya.
Tsawon shekaru 53, shirin ya taimaka wajen haɗa matasan da suka kammala karatun jami’o’i daga sassa daban-daban na ƙasar, tare da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.
Sai dai ministan ya ce bayan shafe shekaru masu yawa ana gudanar da shirin, yin garambawul ya zama wajibi, yana mai cewa: “Buƙatun ƙasarmu sun sauya, kuma mutane da dama na sa ran manufofin shirin NYSC su ma su sauya domin su dace da halin da ake ciki a yanzu.”














