Gwamnatin Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, ya yaba wa dakarun sojin Nijeriya saboda daƙile wani harin ’yan bindiga a Sabon Birni.
A cewar mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ’yan bindigar sun yi yunƙurin kai wa ’yan kasuwa hari yayin da suke tafiya daga ƙauyen Tarah don cin kasuwar mako-mako, amma sojoji suka daƙile harin.
- Ma’aikatar Wajen Sin: Shin Japan Tana Yunkurin Ci Zarafin Sin Tare Da Haifar Da Tashin Hankali
- Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5
Usman, ya ce sojojin sun yi saurin ɗaukar mataki, wanda ya hana afkuwar mummunan hari.
Ya gode wa rundunar sojoji saboda jajircewarsu, tare da kira gare su da su ci gaba da kawar da ’yan ta’adda a Sakkwato da Arewa maso Yamma.
Gwamnan ya kuma roƙi jama’a si riƙa ba da sahihin bayanai ga jami’an tsaro, inda kuma ya yi gargaɗin cewa duk wanda aka kama yans taimaka wa ’yan bindiga zai fuskanci hukunci.
Ya ƙara da cewa Gwamna Ahmed Aliyu zai ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro da duk abin da suke buƙata.














