Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira tiriliyan 9.39 wajen ƙarin albashi, ƙara mafi ƙarancin albashi da kuma biyan alawus-alawus ɗin ma’aikatan gwamnati tsakanin Yunin 2023 zuwa Disamban 2025.
Ministan Kuɗi kuma mai kula da tattalin arziƙin ƙasa, Taiwo Oyedele ne, ya bayyana hakan ranar Laraba a Abuja.
Ya ce kuɗaɗen da ake kashewa kan albashi sun ƙaru ne bayan gwamnatin ta ƙara mafi ƙarancin albashin ƙasa daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000 a shekarar 2024.
Oyedele ya ce sauye-sauyen da gwamnati ta yi, ciki har da cire tallafin man fetur da sauya tsarin musayar kuɗin waje, sun samar da Naira tiriliyan 15.8 ga tarayya a wannan lokacin.
Daga cikin kuɗin, Gwamnatin Tarayya ta samu Naira tiriliyan 5.4, yayin da aka raba Naira tiriliyan 10.4 ga gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi.
Ya ce jimillar ƙarin kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ta samu a wannan lokacin, ciki har da kuɗaɗen sauye-sauye, ƙarin kuɗin shiga da sabbin bashi, sun kai Naira tiriliyan 20.4.
Sai dai ƙarin kuɗin da ta kashe ya kai Naira tiriliyan 30.64.
Baya ga albashi, gwamnati ta kashe Naira tiriliyan 9.37 wajen biyan bashin ƙasashen waje, sannan ta kashe Naira tiriliyan 6.5 kan manyan ayyukan more rayuwa.
Oyedele ya amince cewa sauye-sauyen sun ƙara wa ‘yan Nijeriya matsi, amma ya ce gwamnati ta ɗauki matakai domin rage wa jama’a raɗaɗin matsalar.
Ya ce: “Waɗannan matakai sun zo da tsadar gaske.”














