ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Zata Fara Fasa Wuraren Da Aka Boye Kayan Abinci Ta Sayar

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ta Kafa wani kwamiti na mutane 27 wanda zai tabbatar da abin dokar bunƙasa wadatar abinci da haramta boye shi a jihar.

Hakan yana kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na ofishin sakataren Gwamnatin jihar Katsina, Abdullahi Aliyu Yar’adua ya sanya hannu sannan ya rabawa manema labarai a Katsina.

  • Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Masallata Uku Da Sace Mutane Da Dama A Katsina

Sanarwar ta ce akwai wakilan Kwamishinonin da abin ya shafa da hukumomin tsaro da sarakuna da kwamandojin Hizba da hukumar kiyaye haɗura ta KASSAROTA da wakilan kungiyoyin addini duk acikin kwamitin

ADVERTISEMENT

Sauran sun haɗa da ma’auna da dillalan hatsi da yar tireda da Direbobi da masu motocin haya sai kuma jami’i daga ofishin gwamna wanda zai kasance sakataren kwamitin.

Ayyukan da Kwamitin zai yi sun haɗa da:

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

1. Gano manyan ‘yan kasuwar hatsi da ke faɗin jihar Katsina

2. Faɗakar da su akan illolin ɓoye hatsi da nufin cin ƙazamar riba da yin dukkan abinda kan iya jaza tashin farashin abinci.

3. Gayyato duk masu ruwa da tsaki akan abinda ya shafi farashin abin don bullo da hanyoyin magance matsalar hauhawar farashi.

4. Daidaita farashin hatsi ta hanyar toshe dukkan abinda kan haddasa hauhawar farashin.

5. Sanya ido akan cinikayya da jiglar kayan abincin a cikin jiha da kuma hana fita da shi ta kan iyakokin kasa da ƙasa.

6. Zakulo mutanen da suke ɓoye kayayyakin abinci.

7. Fasa dukkan wurin da aka ɓoye hatsi kana a sayar da shi akan farashin da ya dace.

8. Yin aiki tare da jami’an tsaro wajen ganowa tare da kama duk wanda aka samu ya karya doka.

Ana sa ran cewa za a ƙaddamar da Kwamitin a ranar Laraba, 21/2/2024 a Gidan Gwamnati da ke Katsina da karfe 11 na safe, idan Allah Ya kai mu.

Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Dalilan Da Suka Sa Na Kirkiro Manhajar Sada Zumunta Ta Afrister -Tsohon Dalibin Jami’ar MAAUN

Dalilan Da Suka Sa Na Kirkiro Manhajar Sada Zumunta Ta Afrister -Tsohon Dalibin Jami'ar MAAUN

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.