Ƙungiyar Kwankwasiyya ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan ce-ce-ku-cen da ke tattare da badaƙalar da ake zargin game. Da PFIPC, tana mai cewa lamarin ya wuce batun mutum ɗaya, kuma ya shafi gaskiya, riƙon amana da yadda ake tafiyar da harkokin gwamnati. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar, Habibu Sale Mohammed, ya fitar a ranar Asabar.
Ƙungiyar ta ce duk da cewa Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta wanzuwar PFIPC tare da nesanta kanta da mutanen da ke iƙirarin wakiltarta, rahotannin da ke nuna an ware sama da naira biliyan ɗaya a kasafin kuɗin 2026 ga wata hukuma mai irin wannan suna na buƙatar cikakken bayani ga jama’a. Ta ce dole ne a fayyace yadda aka saka wannan hukuma cikin kasafin kuɗi da kuma waɗanda suka amince da hakan.
Sanarwar ta kuma ce ‘yan Nijeriya na da haƙƙin sanin ko an fitar da kuɗaɗen gwamnati ga wannan hukuma, waɗanne ma’aikatu ko hukumomi suka gudanar da takardun, da kuma yadda ake zargin an yi amfani da takardun bogi na hukuma na tsawon lokaci ba tare da an gano hakan ba. A cewarta, waɗannan tambayoyi ba na siyasa ba ne, sai dai na tabbatar da gaskiya da ɗaukar alhaki wajen amfani da kuɗaɗen jama’a.
Kwankwasiyya ta yi kira ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ta fito da cikakken bayani kan lamarin, tana mai gargadin cewa yin shiru ko kauce wa ɗaukar alhaki zai ƙara rage amincewar jama’a tare da shafar martabar Nijeriya a idanun masu zuba jari.
Haka kuma ta buƙaci Majalisar Dokoki ta Ƙasa, da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin sa ido su gudanar da bincike mai zaman kansa, tana jaddada cewa kowacce naira da aka ware a kasafi mallakin al’ummar Nijeriya ce kuma jama’a sun cancanci sanin gaskiya ba tare da ɓata lokaci ba.














