ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Zazzau

Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli, ya shawarci iyaye su gargaɗi ƴaƴansu da su guji almubazzaranci wajen kashe kuɗaɗe kan kwalliya da aso-ebi a lokacin bukukuwan aurensu.

Da yake jawabi a bikin cika shekaru 20 da kafuwar Crystal Muslim Organisation (CMO) a Abuja ranar Lahadi, sarkin ya ce ya kamata a karkatar da irin waɗannan kuɗaɗe wajen taimaka wa mabuƙata ko kuma a ba ƙungiyoyin da ke tallafa wa talakawa.

Ya nuna damuwarsa cewa duk da matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a ƙasar, iyalai masu hali da dama na ci gaba da kashe maƙudan kuɗaɗe kan abubuwan more rayuwa na alatu, alhali suna yin watsi da buƙatun talakawa. Ya ce wannan na daga cikin abubuwan da ke ƙara haifar da munanan ɗabi’u a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Za ka ga mutane suna kashe miliyoyin Naira kan kayan kwalliya kawai idan za a yi wa yarinya aure, ko kuma su sayi aso-ebi na Naira dubu 500, ko dubu 200, ko dubu 300. A ganina, wannan ba abin karɓa ba ne.”

Ya ƙara da cewa, “Akwai mutane da dama a kan tituna da ba sa iya samun abinci sau uku a rana. Wannan matsala ta yi ƙamari a cikin al’ummarmu. Amma wasu daga cikinmu mun ɗauki matsaya.”

LABARAI MASU NASABA

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

“Ni kaina, ban taɓa kashe ko sisi ɗaya wajen sayen aso-ebi ko kayan kwalliya ga yarinyar da za ta yi aure ba. Idan mahaifiyarta ta ga dama ta yi hakan, wannan ruwanta ne. Ko duk wanda yake so ya yi hakan, ya yi, amma ni ba zan kashe ko sisi ɗaya a kan haka ba.”

Ya ci gaba da cewa, “Ana kashe kuɗaɗe masu yawa a kan bukukuwa waɗanda ba su da wani amfani sosai. Ba na cewa kada a yi biki, amma akwai abubuwan da ya kamata mu rage.”

“Dole ne mu faɗa wa kanmu gaskiya. Ba ma buƙatar irin waɗannan abubuwa, idan aka yi la’akari da halin da ƙasar ke ciki a yanzu.”

Ya ƙara da cewa, “Saboda haka ina roƙon ku da ku mai da hankali kan abubuwan da za su inganta rayuwarku, su sa ku dogaro da kanku, kuma su ƙarfafa haɗin kai a cikin al’umma.”

“Domin idan kai kana rayuwa cikin jin daɗi, alhali mutanen da ke kewaye da kai ba sa iya samun abinci sau uku a rana, to ina ganin akwai matsala. Wannan ne kuma ke jefa al’ummarmu cikin haɗari.”

Sarkin ya kuma yi kira da a haɗa koyar da sana’o’i a cikin manhajojin makarantun boko da na addinin Musulunci domin ɗalibai su samu damar dogaro da kansu bayan sun kammala karatu, tare da kafa ƙananan sana’o’i daga abin da suka koya.

Haka kuma, ya buƙaci matasa a faɗin ƙasar da su rungumi fasaha da zamani domin inganta rayuwar al’umma.

Ya kuma roƙi shugabannin siyasa da su dawo da shirye-shiryen bayar da guraben karatu domin taimaka wa masu buƙata su samu ilimin da iyayensu ba za su iya ɗaukar nauyinsa ba.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙasa na Crystal Muslim Organisation (CMO), Alhaji Muhammad Sagir Shettima, ya ce an shirya taron ne domin bikin cika shekaru 20 da kafuwar ƙungiyar wajen yaɗa koyarwar Musulunci da kuma taimaka wa mabuƙata.

Ya ƙara da cewa, a yayin taron an kuma karrama ɗalibai 12 da suka yi fice a gasar rubutun muƙala ta ƙungiyar, inda aka ba su kyaututtukan kuɗi daban-daban.

Ya yi kira ga Musulmi da su ƙara bayar da sadaka domin tallafa wa talakawa, yana mai cewa ƙungiyar na ba da taimako ga mabuƙata, amma tana buƙatar ƙarin goyon baya domin ta samu damar kai taimako ga mutane da yawa.

Zazzau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
Labarai

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
Zazzau
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Zazzau
Labarai

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026
Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
An Sanya Wuraren Sana’ar Kayan Tangaran Na Jingdezhen Cikin Jerin Wuraren Tarihi Na Duniya Na UNESCO

An Sanya Wuraren Sana’ar Kayan Tangaran Na Jingdezhen Cikin Jerin Wuraren Tarihi Na Duniya Na UNESCO

July 25, 2026
Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.