ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Zazzau

Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli, ya shawarci iyaye su gargaɗi ƴaƴansu da su guji almubazzaranci wajen kashe kuɗaɗe kan kwalliya da aso-ebi a lokacin bukukuwan aurensu.

Da yake jawabi a bikin cika shekaru 20 da kafuwar Crystal Muslim Organisation (CMO) a Abuja ranar Lahadi, sarkin ya ce ya kamata a karkatar da irin waɗannan kuɗaɗe wajen taimaka wa mabuƙata ko kuma a ba ƙungiyoyin da ke tallafa wa talakawa.

Ya nuna damuwarsa cewa duk da matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a ƙasar, iyalai masu hali da dama na ci gaba da kashe maƙudan kuɗaɗe kan abubuwan more rayuwa na alatu, alhali suna yin watsi da buƙatun talakawa. Ya ce wannan na daga cikin abubuwan da ke ƙara haifar da munanan ɗabi’u a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Za ka ga mutane suna kashe miliyoyin Naira kan kayan kwalliya kawai idan za a yi wa yarinya aure, ko kuma su sayi aso-ebi na Naira dubu 500, ko dubu 200, ko dubu 300. A ganina, wannan ba abin karɓa ba ne.”

Ya ƙara da cewa, “Akwai mutane da dama a kan tituna da ba sa iya samun abinci sau uku a rana. Wannan matsala ta yi ƙamari a cikin al’ummarmu. Amma wasu daga cikinmu mun ɗauki matsaya.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

“Ni kaina, ban taɓa kashe ko sisi ɗaya wajen sayen aso-ebi ko kayan kwalliya ga yarinyar da za ta yi aure ba. Idan mahaifiyarta ta ga dama ta yi hakan, wannan ruwanta ne. Ko duk wanda yake so ya yi hakan, ya yi, amma ni ba zan kashe ko sisi ɗaya a kan haka ba.”

Ya ci gaba da cewa, “Ana kashe kuɗaɗe masu yawa a kan bukukuwa waɗanda ba su da wani amfani sosai. Ba na cewa kada a yi biki, amma akwai abubuwan da ya kamata mu rage.”

“Dole ne mu faɗa wa kanmu gaskiya. Ba ma buƙatar irin waɗannan abubuwa, idan aka yi la’akari da halin da ƙasar ke ciki a yanzu.”

Ya ƙara da cewa, “Saboda haka ina roƙon ku da ku mai da hankali kan abubuwan da za su inganta rayuwarku, su sa ku dogaro da kanku, kuma su ƙarfafa haɗin kai a cikin al’umma.”

“Domin idan kai kana rayuwa cikin jin daɗi, alhali mutanen da ke kewaye da kai ba sa iya samun abinci sau uku a rana, to ina ganin akwai matsala. Wannan ne kuma ke jefa al’ummarmu cikin haɗari.”

Sarkin ya kuma yi kira da a haɗa koyar da sana’o’i a cikin manhajojin makarantun boko da na addinin Musulunci domin ɗalibai su samu damar dogaro da kansu bayan sun kammala karatu, tare da kafa ƙananan sana’o’i daga abin da suka koya.

Haka kuma, ya buƙaci matasa a faɗin ƙasar da su rungumi fasaha da zamani domin inganta rayuwar al’umma.

Ya kuma roƙi shugabannin siyasa da su dawo da shirye-shiryen bayar da guraben karatu domin taimaka wa masu buƙata su samu ilimin da iyayensu ba za su iya ɗaukar nauyinsa ba.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙasa na Crystal Muslim Organisation (CMO), Alhaji Muhammad Sagir Shettima, ya ce an shirya taron ne domin bikin cika shekaru 20 da kafuwar ƙungiyar wajen yaɗa koyarwar Musulunci da kuma taimaka wa mabuƙata.

Ya ƙara da cewa, a yayin taron an kuma karrama ɗalibai 12 da suka yi fice a gasar rubutun muƙala ta ƙungiyar, inda aka ba su kyaututtukan kuɗi daban-daban.

Ya yi kira ga Musulmi da su ƙara bayar da sadaka domin tallafa wa talakawa, yana mai cewa ƙungiyar na ba da taimako ga mabuƙata, amma tana buƙatar ƙarin goyon baya domin ta samu damar kai taimako ga mutane da yawa.

Zazzau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Zazzau

Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.