ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

by Rabi'u Ali Indabawa
1 day ago
Zazzau

Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli, ya shawarci iyaye su gargaɗi ƴaƴansu da su guji almubazzaranci wajen kashe kuɗaɗe kan kwalliya da aso-ebi a lokacin bukukuwan aurensu.

Da yake jawabi a bikin cika shekaru 20 da kafuwar Crystal Muslim Organisation (CMO) a Abuja ranar Lahadi, sarkin ya ce ya kamata a karkatar da irin waɗannan kuɗaɗe wajen taimaka wa mabuƙata ko kuma a ba ƙungiyoyin da ke tallafa wa talakawa.

Ya nuna damuwarsa cewa duk da matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a ƙasar, iyalai masu hali da dama na ci gaba da kashe maƙudan kuɗaɗe kan abubuwan more rayuwa na alatu, alhali suna yin watsi da buƙatun talakawa. Ya ce wannan na daga cikin abubuwan da ke ƙara haifar da munanan ɗabi’u a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Za ka ga mutane suna kashe miliyoyin Naira kan kayan kwalliya kawai idan za a yi wa yarinya aure, ko kuma su sayi aso-ebi na Naira dubu 500, ko dubu 200, ko dubu 300. A ganina, wannan ba abin karɓa ba ne.”

Ya ƙara da cewa, “Akwai mutane da dama a kan tituna da ba sa iya samun abinci sau uku a rana. Wannan matsala ta yi ƙamari a cikin al’ummarmu. Amma wasu daga cikinmu mun ɗauki matsaya.”

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

“Ni kaina, ban taɓa kashe ko sisi ɗaya wajen sayen aso-ebi ko kayan kwalliya ga yarinyar da za ta yi aure ba. Idan mahaifiyarta ta ga dama ta yi hakan, wannan ruwanta ne. Ko duk wanda yake so ya yi hakan, ya yi, amma ni ba zan kashe ko sisi ɗaya a kan haka ba.”

Ya ci gaba da cewa, “Ana kashe kuɗaɗe masu yawa a kan bukukuwa waɗanda ba su da wani amfani sosai. Ba na cewa kada a yi biki, amma akwai abubuwan da ya kamata mu rage.”

“Dole ne mu faɗa wa kanmu gaskiya. Ba ma buƙatar irin waɗannan abubuwa, idan aka yi la’akari da halin da ƙasar ke ciki a yanzu.”

Ya ƙara da cewa, “Saboda haka ina roƙon ku da ku mai da hankali kan abubuwan da za su inganta rayuwarku, su sa ku dogaro da kanku, kuma su ƙarfafa haɗin kai a cikin al’umma.”

“Domin idan kai kana rayuwa cikin jin daɗi, alhali mutanen da ke kewaye da kai ba sa iya samun abinci sau uku a rana, to ina ganin akwai matsala. Wannan ne kuma ke jefa al’ummarmu cikin haɗari.”

Sarkin ya kuma yi kira da a haɗa koyar da sana’o’i a cikin manhajojin makarantun boko da na addinin Musulunci domin ɗalibai su samu damar dogaro da kansu bayan sun kammala karatu, tare da kafa ƙananan sana’o’i daga abin da suka koya.

Haka kuma, ya buƙaci matasa a faɗin ƙasar da su rungumi fasaha da zamani domin inganta rayuwar al’umma.

Ya kuma roƙi shugabannin siyasa da su dawo da shirye-shiryen bayar da guraben karatu domin taimaka wa masu buƙata su samu ilimin da iyayensu ba za su iya ɗaukar nauyinsa ba.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙasa na Crystal Muslim Organisation (CMO), Alhaji Muhammad Sagir Shettima, ya ce an shirya taron ne domin bikin cika shekaru 20 da kafuwar ƙungiyar wajen yaɗa koyarwar Musulunci da kuma taimaka wa mabuƙata.

Ya ƙara da cewa, a yayin taron an kuma karrama ɗalibai 12 da suka yi fice a gasar rubutun muƙala ta ƙungiyar, inda aka ba su kyaututtukan kuɗi daban-daban.

Ya yi kira ga Musulmi da su ƙara bayar da sadaka domin tallafa wa talakawa, yana mai cewa ƙungiyar na ba da taimako ga mabuƙata, amma tana buƙatar ƙarin goyon baya domin ta samu damar kai taimako ga mutane da yawa.

Zazzau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

MASU ALAKA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.