Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da amincewar Gwamnatin Tarayya na ɗaukar sabbin jami’an ƴansanda 50,000 da kuma dubban sojoji domin ƙarfafa tsaro a faɗin Nijeriya. Ya bayyana hakan ne a jawabin Ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, yana mai cewa tsaro shi ne ginshiƙin dimokuraɗiyya mai ɗorewa.
Tinubu ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnatinsa na yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar. Ya kuma bayyana cewa kasafin kuɗin 2026 ya ware Naira tiriliyan 5.41 domin ɓangaren tsaro, mafi girma da aka taɓa warewa fannin a tarihin ƙasar.
A cewarsa, duk da ƙalubalen da ake fuskanta, an samu ci gaba wajen rage hare-haren ta’addanci, inda ya ce sama da ‘yan ta’adda 13,000 a ka hallaka a shekara guda, yayin da fiye da mutum 124,000 ciki har da mayaƙa da iyalansu suka miƙa wuya tun daga 2023.
Shugaban ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakai masu tsauri domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai gargaɗin ‘yan bindiga, da masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta’addanci da su tuba ko su fuskanci cikakken ƙarfin gwamnati.














Discussion about this post