ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Yanar Gizo Na Kyautata Rayuwar Jama’a

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Abokaina, bari mu yi tunanin abkuwar wani batu: A cikin wani kauye dake wata kasa ta nahiyar Afirka, wani yaro ya kamu da zazzabi da tsakar dare, amma likita ba zai samu damar zuwa gidan yaron cikin gaggawa ba, saboda yana zaune a cikin gari. Amma iyayen yaron ba su damu ba, maimakon haka sai suka bude wata manhaja (APP) dake cikin wayar salula, da rubuta bayanin halin da yaron ke ciki kan APP din. Sa’an nan bayan kimanin minti 10, sai wani karamin jirgin sama maras matuki ya sauka a gaban kofar gidansu, dauke da maganin da yaron ke bukata.

Hakika wannan batun da muka yi tunani ya riga ya zama gaskiya. Wani saurayi dan kasar Zambia mai suna Clivate Maiba ya koyi dabarar amfani da dandalin sarrafa na’urorin zamani a kasar Sin, sa’an nan ya bude wani kamfanin samar da hidimar jinya a kasarsa ta Zambia, inda ake gwada yin amfani da fasahar zamani wajen sarrafa jirgin sama maras matuki, don kai magani, da jini, da alluran rigakafi da ake bukata, ga likitoci da daidaikun mutane da ke zama a yankunan karkara marasa hanyoyi masu inganci.

Wannan misali ya nuna yadda hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar yanar gizo ko Internet da fasahohin zamani ke haifar wa matasan kasashen Afirka damammakin kaddamar da sabbin sana’o’i, sa’an nan an samar da taimako ga masu raunin tattalin arziki dake nahiyar Afirka a fannin kyautata zaman rayuwarsu.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Manyan Bangarori 5

A yau Talata an gudanar da wani dandalin tattauna damar hadin gwiwa kan ci gaban yanar gizo ko Internet, tsakanin bangarorin Afirka da Sin, a birnin Xiamen na kasar Sin, inda jami’ai da ‘yan kasuwa na bangarorin 2 suke mai da hankali kan damar hadin kansu, a fannonin tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani, da kafofin yada labaru na yanar gizo, da tsaron yanar gizo, da fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI, da dai sauransu, gami da tattauna dabarar yin amfani da yanar gizo da fasahohin zamani wajen kyautata zaman rayuwar jama’a, kamar dai yadda misalin kasar Zambia da na gabatar muku ya nuna.

Cikin shekarun nan, an samu dimbin nasarori a hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, a fannin yanar gizo ko Internet. Misali a bangaren gina kayayyakin more rayuwa, ya zuwa karshen shekarar 2021, kasar Sin ta gina fiye da kashi 50% na tashoshi da yanar gizo mai sauri na wayar salula, gami da shimfida kananan wayoyin aika sako ta haske fiye da tsawon kilomita dubu 200, a kasashen Afirka. Kana a fannin ciniki ta yanar gizo, sama da rabi na yawan cinikayyar yanar gizo da ake yi a kasuwannin gabashin Afirka an yi su ne ta dandalin ciniki na Kilimall da wani basine ya kafa, inda yawan mutanen da suke amfani da dandalin ya zarce miliyan 10. Sa’an nan a fannin hada-hadar kudi, kamfanin Opay na kasar Najeriya ya shigar da jari da fasahohi daga kasar Sin, ta yadda ya zama daya daga cikin kamfanonin hidimar biyan kudi mafi girma a kasar Najeriya. A sauran fannoni irinsu horar da ma’aikata, da tsaron yanar gizo ma, ana samun yanayi kusan iri daya. Za a iya cewa a kusan dukkan sana’o’i masu alaka da fasahohin yanar gizo na galibin kasashen dake nahiyar Afirka, ana iya ganin yadda fasahohi da jarin kasar Sin ke taka muhimmiyar rawa.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Za a so a yi tambaya cewa, me ya sa kasar Sin ce ke taka rawa a fannin? Kuma don me ake son hadin gwiwa da kasar Sin, yayin da ake neman raya sana’o’i masu alaka da yanar gizo ko Internet?

Dalilin shi ne, da farko, fasahohin kasar Sin a fannin yanar gizo su ne a kan gaba a duniya.

An kammala aikin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da fasahohin sadarwa mafi girma a duniya, a kasar ta Sin, ta yadda ko a cikin kauyukan kasar ma, ana samun ingantaccen tsarin sadarwa. Ban da haka, kasar ita ta fara rungumar fasahar sadarwa mai ci gaba ta 5G, inda a karshen shekarar 2023, yawan al’ummar kasar masu wayoyin salula dake aiki da 5G ya kai miliyan 805. Ban da haka, kasar Sin ta kware a fannin kirkirar sabbin fasahohi, abin da ya sa ta kan gaba a duniya a fannonin mallakar fasahohi masu alaka da na’urorin kwaikwayon tunanin dan Adam, da aikin tsara karamin kayan latironi na Chip, da dai sauransu.

Kana dalili na biyu shi ne, akidar kasar Sin ta fuskar hadin kai tare da kasashen Afirka ta gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da sakamako na zahiri, ta sa kasar yarda da gabatar da ingantattun fasahohi, da damammakin raya kasa, ga bangarorin Afirka. Cikin shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, da kasar Sin ta gabatar, kasar ta yi alkawarin taimakawa kasashen Afirka wajen gina kayayyakin aikin sadarwa, da kula da yanar gizo, da sayar da kayayyaki ga kasuwannin Sin ta hanyar cinikin yanar gizo, da kuma rage talauci ta hanyar amfani da fasahohin zamani.

Idan muka leka kasar Sin, za mu ga yadda yanar gizo ko Internet ta shafi dukkan bangarorin rayuwar jama’ar kasar, irinsu sayayya, da biyan kudi, da hulda da abokai, da karatu, da ganin likita, da gudanar da taro, da sayar da kayyayaki ta hanyar watsa bidiyo kai tsaye, da dai sauransu. Ta wayar salula, kusan za a iya tafiyar da dukkan al’amuran yau da kullum a kasar. To, wannan irin saukin rayuwa, da saurin ci gaba da fasahohin zamani suke haifarwa tattalin arziki, da zaman al’umma, su ne abubuwan da kasar Sin ke son morewa tare da jama’ar kasashen Afirka, ta hanyar gudanar da hadin gwiwa tsakanin bangarorin 2. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
An Kama Wani Matashi Mai Shekaru 25 Bisa Zargin Kashe Abokinsa A Kano

An Kama Wani Matashi Mai Shekaru 25 Bisa Zargin Kashe Abokinsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.