Kashi na farko na alhazan Jihar Kwara guda 374 sun tashi daga Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 a ranar Laraba.
Alhazan, tare da rakiyar jami’ai biyu na Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) da jami’in gwamnati guda ɗaya daga jihar, sun tashi daga Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idi-Agbon da ke Ilorin cikin jirgin Max Air da misalin ƙarfe 3:00 na dare, zuwa birnin Madina.
Ana sa ran jimillar maniyyata 1,714 daga jihar za su halarci aikin Hajjin bana.
Yayin da yake yi wa alhazan bankwana, Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukace su da su zama jakadu nagari na jihar da Nijeriya baki daya ta hanyar nuna ɗabi’a ta gari da kuma bin dokokin ƙasar Saudiyya yadda ya kamata.
Gwamnan, wanda mai ba shi shawara na musamman, Alhaji Saadu Salaudeen, ya wakilta, ya kuma bukaci alhazan da su yi addu’ar zaman lafiya da haɗin kai a ƙasar nan baki daya.















Discussion about this post