Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano za ta fara jigilar maniyyatan jihar zuwa ƙasar Saudiyya daga ranar 14 ga Mayu, 2026.
Darakta Janar na hukumar, Abubakar Matawalle, ya bayyana hakan ranar Litinin yayin bikin rufe taron horas da maniyyatan da aka gudanar a Makarantar Nazarin Larabci ta Kano, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen aikin Hajjin 2026.
Ya ce, “Bisa jadawalin da Hukumar Nin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta fitar, jirgin farko na Jihar Kano zuwa Saudiyya zai tashi a ranar 14 ga Mayu, 2026, inda Max Air zai fara ɗaukar nauyin jigilar maniyyatan.”
Ya kuma ƙara da cewa hukumar ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da cewa an fara aikin Hajjin cikin sauƙi da nasara.















Discussion about this post