Masanin tattalin arziki na kasar Madagascar Hugues Rajeon, ya ce manufar Sin ta soke haraji baki daya kan hajojin kasashen Afirka, za ta samar da muhimmiyar dama ga kasashen nahiyar wajen daga matsayin kayayyakinsu a tsarin ciniki na duniya, tare da samar da gudummawa wajen zamanantar da tattalin arzikin nahiyar baki daya.Tun daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin ta fara aiwatar da manufar, kan hajojin kasashen Afirka 53 da ke da huldar diplomasiyya da ita.
A ganin masanin, a shekarun baya-baya nan, kasashen Afirka sun fi sha’awar kasuwar kasar Sin. Kuma bisa wannan yanayi, kasar Sin ta dauki manufar soke haraji don nuna goyon baya ga ci gaban nahiyar Afirka.
Ya ce, manufar za ta sa kaimi ga fitar da kayayyakin Afirka zuwa kasar Sin, da kyautata zaman rayuwar jama’ar Afirka, kana za ta inganta hadin gwiwar kamfanonin samar da kaya na Afirka da kamfanonin kasar Sin, da sa kaimi ga raya kamfanonin Afirka baki daya.Ya kara da cewa, kasar Sin tana da masu sayayya masu tarin yawa, da ke da bukatu iri daban daban, kuma kasuwar kasar Sin na da kyakkyawar makoma, haka kuma manufar soke haraji ta kasar Sin za ta inganta karfin kayayyakin Afrika a fannonin farashi da takara a kasuwar duniya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post