ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kwastam Ta Kama Haramtattun Kaya Da Kudinsu Ya Kai Naira Miliyan 91.5 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar Kwastam ta Nijeriya, ta kama wasu kayayyaki da ake zargin an yi fasakwaurinsu ne da kudinsu ya kai Naira miliyan 91.5 a Kebbi.

Sabon shugaban hukumar a jihar, Mista Ben Oramalugo ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar na tsawon makonni biyu da suka gabata a Birnin Kebbi.

Kwastam
Ya ce nasarar da aka samu na kwace kayayyakin ta biyo bayan umarnin da ya bayar ga jami’an da ke sanya ido a kan manyan iyakokin da ke cikin jihar bayan ya karbi ragamar mulki a ranar 1 ga watan Fabarairu.

ADVERTISEMENT

“Kokari da jami’an rudunar ke yi ya samar da sakamako mai kyau a ayyukan yaki da fasa-kwauri a jihar. A tsawon lokacin, mun sami nasarar kama wasu abubuwa daban daban har guda 14.

  • 2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

 

“Kayayyakin sun hada da Lita 8,975 na man fetur da aka loda a cikin jarka mai cin lita 25, buhunan shinkafar kasar waje 189, buhunan sukari 71 da aka shigo da su kasar waje, da dilolin gwanjo 42 da buhu 36 na takalman da aka yi amfani da su.

Kwastam
“Sauran sun hada da, kwali 74 na man sauya launin fata, batir mai amfani da hasken rana 110, katan-katan na magunguna 105, motoci bakwai da aka yi amfani da su wajen jigilar kayayyaki da kuma motar tanka daya da ake tsare da su. Kudin kayayyakin da aka ambata ya kai Naira miliyan 91.5,” in ji shi.

Har ilayau, mista Ben Oramalugo ya ce duk da irin makudan kudi da gwamnati ta biya domin samar da man fetur ga ’yan kasa a kan farashi mai sauki, wasu marasa kishin kasa sun zabi karkatar da kayan zuwa kasashen makwabta don amfanin kansu da kuma azurta kansu.

Ya kara da cewa, “Rundunar tana da duk wani kayan aiki da hukumar gudanarwar hukumar ta bayar a karkashin jagorancin Kanar Hamid Ibraheem-Ali, domin gudanar da aikinta kamar yadda dokar hukumar kwastam (CEMA) ta CAP C45 LFN, 2004 ta tanada.

Kwastam
“Musamman, sashe na 167 ya ba mu ikon kwace kayayyakin da aka shigo da su ba bisa ka’ida ba wanda ya saba wa dokokin da ba su dace ba,” in ji shi.

Bugu da kari mista Oramalugo ya ci gaba da bayyana cewa, hukumar ta gudanar da ayyukan hana fasa-kwauri don kare masana’antu na cikin gida da kuma karfafa tsaron iyakokin kasar domin ka da ‘yan ta’adda su shigo kasar.

Kwastam
“Ina so in yi amfani da wannan kafar wajen mika godiyarmu ga hukumomin ‘yan’uwanmu, da sauran sassan ma’aikata bisa goyon bayan da suke bayarwa da hadin gwiwar juna ta hanyar musayar bayanan sirri ga aikinmu na tabbatar da tsaron kasa.

Kwanturolan na Kwastam, ya yi godiya ga masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen gudanar da ayyukansu.

Kwastam
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.