• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kwastam Ta Kama Haramtattun Kaya Da Kudinsu Ya Kai Naira Miliyan 91.5 A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Hukumar Kwastam Ta Kama Haramtattun Kaya Da Kudinsu Ya Kai Naira Miliyan 91.5 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kwastam ta Nijeriya, ta kama wasu kayayyaki da ake zargin an yi fasakwaurinsu ne da kudinsu ya kai Naira miliyan 91.5 a Kebbi.

Sabon shugaban hukumar a jihar, Mista Ben Oramalugo ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar na tsawon makonni biyu da suka gabata a Birnin Kebbi.

Kwastam
Ya ce nasarar da aka samu na kwace kayayyakin ta biyo bayan umarnin da ya bayar ga jami’an da ke sanya ido a kan manyan iyakokin da ke cikin jihar bayan ya karbi ragamar mulki a ranar 1 ga watan Fabarairu.

“Kokari da jami’an rudunar ke yi ya samar da sakamako mai kyau a ayyukan yaki da fasa-kwauri a jihar. A tsawon lokacin, mun sami nasarar kama wasu abubuwa daban daban har guda 14.

  • 2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

 

Labarai Masu Nasaba

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

 

“Kayayyakin sun hada da Lita 8,975 na man fetur da aka loda a cikin jarka mai cin lita 25, buhunan shinkafar kasar waje 189, buhunan sukari 71 da aka shigo da su kasar waje, da dilolin gwanjo 42 da buhu 36 na takalman da aka yi amfani da su.

Kwastam
“Sauran sun hada da, kwali 74 na man sauya launin fata, batir mai amfani da hasken rana 110, katan-katan na magunguna 105, motoci bakwai da aka yi amfani da su wajen jigilar kayayyaki da kuma motar tanka daya da ake tsare da su. Kudin kayayyakin da aka ambata ya kai Naira miliyan 91.5,” in ji shi.

Har ilayau, mista Ben Oramalugo ya ce duk da irin makudan kudi da gwamnati ta biya domin samar da man fetur ga ’yan kasa a kan farashi mai sauki, wasu marasa kishin kasa sun zabi karkatar da kayan zuwa kasashen makwabta don amfanin kansu da kuma azurta kansu.

Ya kara da cewa, “Rundunar tana da duk wani kayan aiki da hukumar gudanarwar hukumar ta bayar a karkashin jagorancin Kanar Hamid Ibraheem-Ali, domin gudanar da aikinta kamar yadda dokar hukumar kwastam (CEMA) ta CAP C45 LFN, 2004 ta tanada.

Kwastam
“Musamman, sashe na 167 ya ba mu ikon kwace kayayyakin da aka shigo da su ba bisa ka’ida ba wanda ya saba wa dokokin da ba su dace ba,” in ji shi.

Bugu da kari mista Oramalugo ya ci gaba da bayyana cewa, hukumar ta gudanar da ayyukan hana fasa-kwauri don kare masana’antu na cikin gida da kuma karfafa tsaron iyakokin kasar domin ka da ‘yan ta’adda su shigo kasar.

Kwastam
“Ina so in yi amfani da wannan kafar wajen mika godiyarmu ga hukumomin ‘yan’uwanmu, da sauran sassan ma’aikata bisa goyon bayan da suke bayarwa da hadin gwiwar juna ta hanyar musayar bayanan sirri ga aikinmu na tabbatar da tsaron kasa.

Kwanturolan na Kwastam, ya yi godiya ga masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen gudanar da ayyukansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyar Da Sin Take Bi Wajen Bunkasa Aikin Gona Za Ta Baiwa Duk Fadin Duniya Kwarin Gwiwa

Next Post

Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

Related

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

33 minutes ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 hour ago
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

15 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

16 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

16 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

17 hours ago
Next Post
Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

LABARAI MASU NASABA

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.