ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kwastam Ta Kama Haramtattun Kaya Da Kudinsu Ya Kai Naira Miliyan 91.5 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar Kwastam ta Nijeriya, ta kama wasu kayayyaki da ake zargin an yi fasakwaurinsu ne da kudinsu ya kai Naira miliyan 91.5 a Kebbi.

Sabon shugaban hukumar a jihar, Mista Ben Oramalugo ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar na tsawon makonni biyu da suka gabata a Birnin Kebbi.

Kwastam
Ya ce nasarar da aka samu na kwace kayayyakin ta biyo bayan umarnin da ya bayar ga jami’an da ke sanya ido a kan manyan iyakokin da ke cikin jihar bayan ya karbi ragamar mulki a ranar 1 ga watan Fabarairu.

ADVERTISEMENT

“Kokari da jami’an rudunar ke yi ya samar da sakamako mai kyau a ayyukan yaki da fasa-kwauri a jihar. A tsawon lokacin, mun sami nasarar kama wasu abubuwa daban daban har guda 14.

  • 2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

 

LABARAI MASU NASABA

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

 

“Kayayyakin sun hada da Lita 8,975 na man fetur da aka loda a cikin jarka mai cin lita 25, buhunan shinkafar kasar waje 189, buhunan sukari 71 da aka shigo da su kasar waje, da dilolin gwanjo 42 da buhu 36 na takalman da aka yi amfani da su.

Kwastam
“Sauran sun hada da, kwali 74 na man sauya launin fata, batir mai amfani da hasken rana 110, katan-katan na magunguna 105, motoci bakwai da aka yi amfani da su wajen jigilar kayayyaki da kuma motar tanka daya da ake tsare da su. Kudin kayayyakin da aka ambata ya kai Naira miliyan 91.5,” in ji shi.

Har ilayau, mista Ben Oramalugo ya ce duk da irin makudan kudi da gwamnati ta biya domin samar da man fetur ga ’yan kasa a kan farashi mai sauki, wasu marasa kishin kasa sun zabi karkatar da kayan zuwa kasashen makwabta don amfanin kansu da kuma azurta kansu.

Ya kara da cewa, “Rundunar tana da duk wani kayan aiki da hukumar gudanarwar hukumar ta bayar a karkashin jagorancin Kanar Hamid Ibraheem-Ali, domin gudanar da aikinta kamar yadda dokar hukumar kwastam (CEMA) ta CAP C45 LFN, 2004 ta tanada.

Kwastam
“Musamman, sashe na 167 ya ba mu ikon kwace kayayyakin da aka shigo da su ba bisa ka’ida ba wanda ya saba wa dokokin da ba su dace ba,” in ji shi.

Bugu da kari mista Oramalugo ya ci gaba da bayyana cewa, hukumar ta gudanar da ayyukan hana fasa-kwauri don kare masana’antu na cikin gida da kuma karfafa tsaron iyakokin kasar domin ka da ‘yan ta’adda su shigo kasar.

Kwastam
“Ina so in yi amfani da wannan kafar wajen mika godiyarmu ga hukumomin ‘yan’uwanmu, da sauran sassan ma’aikata bisa goyon bayan da suke bayarwa da hadin gwiwar juna ta hanyar musayar bayanan sirri ga aikinmu na tabbatar da tsaron kasa.

Kwanturolan na Kwastam, ya yi godiya ga masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen gudanar da ayyukansu.

Kwastam
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

LABARAI MASU NASABA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.