ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

by Sadiq
11 months ago
Jonathan

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya gargaɗi tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan da kada ya sake ya fito takarar shugabancin ƙasa a 2027.

A cewar Shehu Sani, idan Jonathan ya amince ya tsaya takara, zai iya rasa mutuncin da yake da shi a Nijeriya da ma ƙasashen waje.

  • Amurka Ta Yaba Da Nasarar Nijeriya Wajen Kama Shugabannin Ansaru
  • PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

Ya ce a baya, musamman a zaɓukan 2019 da 2023, an yi ƙoƙarin tursasa wa Jonathan ya tsaya takara, amma ya ƙi saboda ya san hatsarin da hakan zai iya jawo masa wajen kare martabarsa.

ADVERTISEMENT

Shehu Sani ya ƙara da cewa jam’iyyar PDP da ta kawo Jonathan mulki a baya ba ita ce irin wadda ya sani ba a yanzu, saboda rikice-rikice da rabuwar kawuna sun yi mata yawa.

“Yanzu PDP ta yi rauni sosai, hatta wasu ‘yan majalisa da gwamnoninta sun koma APC. A ganinmu Jonathan ya fi dacewa ya ci gaba da zama shugaba da ake daraja shi a gida da waje, ba tare da sake tsayawa takara ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Ya kuma yi nuni da cewa ko da PDP na son amfani da Jonathan don ta dawo da ƙarfinta, ba zai yiwu ya warware matsalolin da jam’iyyar ke ciki shi kaɗai ba.

Dangane da ra’ayin da wasu ke yi. A cewa Jonathan na iya kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu idan ya tsaya takara, Shehu Sani ya ce ba ya ganin hakan zai yiwu.

“Jonathan ya riga ya yi nasa lokacin, kuma mutane suna girmama shi a yanzu. Abin da ya rage masa shi ne ya kiyaye wannan daraja, kar ya ɓata ta, ta hanyar sake tsayawa takara,” a cewarsa.

Jonathan dai ya daina shiga harkokin siyasa tun bayan da ya faɗi zaɓe a hannun tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari a 2015, amma PDP ta tabbatar da cewa tana tattaunawa da shi kan yiwuwar ya tsaya mata takara a 2027.

MASU ALAKA

inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Next Post
Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi

Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.