Tauraron ɗan wasan gaban ƙungiyar Santos FC, Neymar Jr, ya bayyana cewa yana tunanin yin ritaya daga buga ƙwallon ƙafa a ƙarshen shekarar nan. Ɗan wasan mai shekaru 34 har yanzu shi ne mafi tsada a tarihin saye da sayarwa, bayan Paris Saint-Germain ta biya Yuro miliyan 200 a 2017 domin ɗauko shi.
Neymar ya sha fama da raunuka a ‘yan shekarun baya-bayan nan, amma yana fatan buga Gasar Kofin Duniya na 2026 tare da ƙasarsa ta Brazil. A watan Janairun 2025 ya koma Santos daga Al Hilal SFC, inda ya tsawaita kwantiraginsa har zuwa ƙarshen 2026.
- Ramadan: Kano Ta Bayar Da Umarnin Rufe Wuraren DJ Da Tarukan Nishaɗantarwa
- Tsarin Siyasar Kano: Ya Kamata Gwamna Abba Ya Yunkura…
Sai dai raunukan da ya sha, ciki har da tiyatar gwuiwa da aka yi masa a ƙarshen Disambar bara, sun sa ya rasa gurbi a tawagar ƙasar na ɗan lokaci, duk da cewa ya dawo wasa a makon da ya gabata.
A wata hira da ya yi da tashar yanar gizo ta Brazil Caze, Neymar ya ce: “Ban san abin da zai faru daga yanzu ba, ban san me zai faru a shekara mai zuwa ba. Watakila idan watan Disamba ya zo in yi ritaya.” A halin yanzu, shi ne kan gaba a tarihin masu zura ƙwallaye a tawagar Brazil da ƙwallaye 79, biyu fiye da Pelé.















Discussion about this post