Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta sanar da sake fara aikin Rijistar Masu Zaɓe (CVR) a faɗin ƙasa daga ranar Litinin 11 ga Mayu zuwa Juma’a 10 ga Yuli, 2026, a matsayin mataki na uku kuma na ƙarshe na wannan shiri.
A wata sanarwa da shugaban kwamitin wayar da kan masu zabe, Mohammed Kudu Haruna, ya fitar, ya ce an dakatar da aikin ne tun a ranar 17 ga Afrilu domin bai wa hukumar damar gyara kundin masu zaɓe bayan kammala karɓar ƙorafe-ƙorafe da gyare-gyare daga jama’a.
Hukumar ta buƙaci ’yan Nijeriya da suka kai shekaru 18 da haihuwa ko kuma waɗanda ba su samu damar yin rijista a baya ba da su yi anfani da wannan dama, tare da jaddada cewa waɗanda ke son gyara bayanansu, canja wurin rajista ko neman sabon katin zabe (PVC) za su iya yin hakan ta hanyar shafin yanar gizo na INEC ko ofisoshinta a jihohi da ƙananan hukumomi.
INEC ta kuma bayyana cewa za a baje kundin masu zaɓe domin dubawa daga ranar 23 zuwa 29 ga Yuli, 2026, domin bai wa jama’a damar tabbatar da sahihancin bayanan da kuma gabatar da ƙorafe-ƙorafe idan akwai kura-kurai.
Hukumar ta tabbatar da cewa ta kammala dukkan shirye-shirye don gudanar da aikin cikin nasara, tare da kira ga al’umma da su fito kwansu da kwarkwata domin ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya.















Discussion about this post