Tsohon Ministan Sadarwa kuma mai neman takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC, Farfesa Isa Ali Pantami, ya sha alwashin bin duk hanyoyin doka domin ƙalubalantar zaɓin ɗan takarar gwamna bisa tsarib masalaha (consensus) da aka yi a Jihar Gombe, yana mai cewa tsarin bai bi ƙa’ida ba.
Rikicin ya biyo bayan sanarwar da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya yi na ayyana Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar ta hanyar yarjejeniya bayan taron masu ruwa da tsaki. Sai dai Pantami, a wata hira da BBC Hausa, ya ce abin da aka yi ba zai iya zama sahihiyar yarjejeniya ba.
A cewarsa, duk wani tsarin yarjejeniya dole ne ya samu amincewar dukkan masu ruwa da tsaki, ciki har da waɗanda ba su halarta ba ta hanyar wakilci, sannan kuma ya dace da doka sharuɗɗan da ya ce ba a cika su ba. Ya ƙara da cewa ba a taɓa nuna musu ƙa’idojin da za a bi wajen aiwatar da yarjejeniyar ba.
Pantami ya kuma zargi rashin gaskiya wajen gayyatar taron da aka yanke hukuncin, yana mai cewa an ba su sanarwa cikin gajeren lokaci wanda bai ba su damar halarta ba. Ya jaddada cewa ya fi amincewa da zaɓen fidda gwani kai tsaye (direct primary), yana mai cewa wannan hanya ce da ke nuna goyon bayan ’yan jam’iyya a matakin ƙasa.
Ya kammala da cewa abin da yake nema shi ne adalci, yana gargaɗin cewa duk wani zalunci za a ƙalubalance shi har zuwa mataki mafi girma na shari’a, tare da tabbatar da cewa za a yi gwagwarmaya mai ƙarfi domin tabbatar da gaskiya a cikin jam’iyyar.















Discussion about this post