Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai wani hari cikin dare na hadin kai kan wasu al’ummomi da dama a Jihar Kebbi, inda suka kone gidaje tare da janyo asarar rayuka da ba a bayyana adadinsu ba.
Harin ya faru ne a daren Lahadi, lokacin da maharan dauke da makamai suka kai farmaki kan ƙauyuka da suka haɗa da Gebe, Kawara da Kalkami a ƙaramar hukumar Shanga.
- Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara
- Ɗimbin Magoya Bayan Jam’iyyun APC, NNPP Da PDP Sun Koma ADC A Jihar Jigawa
Shaidun gani da ido da majiyoyin yankin sun bayyana cewa, maharan sun banka wa gidaje da dama wuta, lamarin da ya tilasta mazauna garuruwan tserewa domin tsira da rayukansu.
Majiyoyin tsaro sun nuna cewa ana zargin maharan sun fito ne daga maboyarsu a dajin Wawa da ke Jihar Neja, wani yanki da aka daɗe ana danganta shi da ayyukan ’yan bindiga kuma yana kusa da wuraren da abin ya shafa.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin, rundunar ’yansandan Jihar Kebbi ta bayyana lamarin a matsayin harin hadin kai.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Bashir Usman, ya ce an tura jami’an tsaro zuwa yankin domin kwantar da hankula.















Discussion about this post