Kotun Daukaka Kara ta Tarayya dake Kaduna ta Kori takardar daukaka karar da lauyoyin Alhaji Mahmood Sani Sha’aban, suka shigar na a dakatar da hukuncin da wata Babbar kotun Jihar ta yanke na bada umurnin yin gwanjon wasu kadarorin Hon. Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa bisa rashin cika sharudda.
Da farko dai lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta gabatar da takardar daukaka karar dake neman dakatarwa da kara wa’adin hukuncin da babbar kotun baya ta yanke don baiwa wanda suke wakilta damar biyan kudaden da kansa a maimakon a bar ma Wanda ke bin bashin damar yin gwanjon.
Sai dai a na shi bangaren, lauya mai kare wanda Ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya janyo hankalin kotun kan cewa masu karar sun saba ka’ida tun daga kan lokacin shigar da karar da rashin cika wasu ka’idoji na gabatar da takardar daukaka karar, da rashi mutunta umurnin da Babbar kotun baya ta yanke a kan lokacin da ya kamata a biya bashin.
Sannan Mista Abdullahi Yahya SAN ya nemi kotun da ta sa Masu Kara su biyasu diyar rabin miliyan sakamakon bata lokacin da rashin cimma umurnin kotun baya.
Bayan sauraron bangarorin biyu, Justice Onyekachi Aja Otisi ta kotun daukaka karar ta Tarayya, ta kori takardar daukaka karar da lauya mai kare Wanda ke kara ta shigar, bisa rashin cika ka’idoji shigar da karar a kotun daukaka karar ta tarayya dake Kaduna, sannan ta nemi ya biya tarar naira dubu dari biyu ga masu karar kamar yadda lauyan mai kare wanda ake karar ya nema.
Da yake karin bayani game da wannan Zama lauyan wanda ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya ce, da wannan korar karar da aka yi, ya Basu damar Cigaba da aiki da wancan hukuncin da kotun bayan ta yanke na yin gwanjon wasu daga cikin kadarorin Hon. Mahmood Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa.
A nata bangaren lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta tabbatar da cewa rashin cika wasu daga cikin ka’idojin shigar da karar a kotun daukaka karar ya sa aka kori karar.
Ita dai wannan shari’ar ta samo asali ne daga wata yarjejeniyar bashi da aka sanya wa hannu a shekarar 2018 tsakanin Hon. Sani Mahmood Sha’aban (Dan Buran Zazzau) da Alhaji Umar Faruk Abdullahi domin taimaka wa Sha’aban ya samu ‘yanci daga matsalar kama shi da tsare shi da akayi a gidan yari a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), a wancan shekarar.
An ba Sha’aban bashin dala miliyan ɗaya na Amurka ($1,000,000) da kuma naira miliyan 11.2 ba tare da riba ko ruwa ba, bisa tanade-tanaden shari’ar Musulunci, tare da sharadin cewa zai mayar da bashin cikin watanni shida.
Lauyoyin Sha’aban ne suka tsara tare da shaida yarjejeniyar, sannan ɗansa ya sanya hannu a madadinsa kafin daga bisani, bayan dawowarsa daga gidan yari, shi ma ya sanya hannu domin amincewa da ita.
Sha’aban ya riga ya fara biyan chabar kudi har dala $290,762 daga cikin bashin dala miliyan ɗaya, amma daga baya ya ƙi biyan ragowar bashin. Daya daga cikin sharuɗɗan yarjejeniyar ita ce a biya bashin cikin watanni shida tare da mayar da shi da irin kuɗin da aka karɓa da su.















Discussion about this post