ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

by Bello Hamza and Sulaiman
3 weeks ago
Kotu

Kotun Daukaka Kara ta Tarayya dake Kaduna ta Kori takardar daukaka karar da lauyoyin Alhaji Mahmood Sani Sha’aban, suka shigar na a dakatar da hukuncin da wata Babbar kotun Jihar ta yanke na bada umurnin yin gwanjon wasu kadarorin Hon. Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa bisa rashin cika sharudda.

Da farko dai lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta gabatar da takardar daukaka karar dake neman dakatarwa da kara wa’adin hukuncin da babbar kotun baya ta yanke don baiwa wanda suke wakilta damar biyan kudaden da kansa a maimakon a bar ma Wanda ke bin bashin damar yin gwanjon.

Sai dai a na shi bangaren, lauya mai kare wanda Ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya janyo hankalin kotun kan cewa masu karar sun saba ka’ida tun daga kan lokacin shigar da karar da rashin cika wasu ka’idoji na gabatar da takardar daukaka karar, da rashi mutunta umurnin da Babbar kotun baya ta yanke a kan lokacin da ya kamata a biya bashin.

ADVERTISEMENT

Sannan Mista Abdullahi Yahya SAN ya nemi kotun da ta sa Masu Kara su biyasu diyar rabin miliyan sakamakon bata lokacin da rashin cimma umurnin kotun baya.

Bayan sauraron bangarorin biyu, Justice Onyekachi Aja Otisi ta kotun daukaka karar ta Tarayya, ta kori takardar daukaka karar da lauya mai kare Wanda ke kara ta shigar, bisa rashin cika ka’idoji shigar da karar a kotun daukaka karar ta tarayya dake Kaduna, sannan ta nemi ya biya tarar naira dubu dari biyu ga masu karar kamar yadda lauyan mai kare wanda ake karar ya nema.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Da yake karin bayani game da wannan Zama lauyan wanda ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya ce, da wannan korar karar da aka yi, ya Basu damar Cigaba da aiki da wancan hukuncin da kotun bayan ta yanke na yin gwanjon wasu daga cikin kadarorin Hon. Mahmood Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa.

A nata bangaren lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta tabbatar da cewa rashin cika wasu daga cikin ka’idojin shigar da karar a kotun daukaka karar ya sa aka kori karar.

Ita dai wannan shari’ar ta samo asali ne daga wata yarjejeniyar bashi da aka sanya wa hannu a shekarar 2018 tsakanin Hon. Sani Mahmood Sha’aban (Dan Buran Zazzau) da Alhaji Umar Faruk Abdullahi domin taimaka wa Sha’aban ya samu ‘yanci daga matsalar kama shi da tsare shi da akayi a gidan yari a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), a wancan shekarar.

An ba Sha’aban bashin dala miliyan ɗaya na Amurka ($1,000,000) da kuma naira miliyan 11.2 ba tare da riba ko ruwa ba, bisa tanade-tanaden shari’ar Musulunci, tare da sharadin cewa zai mayar da bashin cikin watanni shida.

Lauyoyin Sha’aban ne suka tsara tare da shaida yarjejeniyar, sannan ɗansa ya sanya hannu a madadinsa kafin daga bisani, bayan dawowarsa daga gidan yari, shi ma ya sanya hannu domin amincewa da ita.

Sha’aban ya riga ya fara biyan chabar kudi har dala $290,762 daga cikin bashin dala miliyan ɗaya, amma daga baya ya ƙi biyan ragowar bashin. Daya daga cikin sharuɗɗan yarjejeniyar ita ce a biya bashin cikin watanni shida tare da mayar da shi da irin kuɗin da aka karɓa da su.

Kotu
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa
  • Sulaiman
    Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.