ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

by Bello Hamza and Sulaiman
2 hours ago
Kotu

Kotun Daukaka Kara ta Tarayya dake Kaduna ta Kori takardar daukaka karar da lauyoyin Alhaji Mahmood Sani Sha’aban, suka shigar na a dakatar da hukuncin da wata Babbar kotun Jihar ta yanke na bada umurnin yin gwanjon wasu kadarorin Hon. Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa bisa rashin cika sharudda.

Da farko dai lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta gabatar da takardar daukaka karar dake neman dakatarwa da kara wa’adin hukuncin da babbar kotun baya ta yanke don baiwa wanda suke wakilta damar biyan kudaden da kansa a maimakon a bar ma Wanda ke bin bashin damar yin gwanjon.

Sai dai a na shi bangaren, lauya mai kare wanda Ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya janyo hankalin kotun kan cewa masu karar sun saba ka’ida tun daga kan lokacin shigar da karar da rashin cika wasu ka’idoji na gabatar da takardar daukaka karar, da rashi mutunta umurnin da Babbar kotun baya ta yanke a kan lokacin da ya kamata a biya bashin.

ADVERTISEMENT

Sannan Mista Abdullahi Yahya SAN ya nemi kotun da ta sa Masu Kara su biyasu diyar rabin miliyan sakamakon bata lokacin da rashin cimma umurnin kotun baya.

Bayan sauraron bangarorin biyu, Justice Onyekachi Aja Otisi ta kotun daukaka karar ta Tarayya, ta kori takardar daukaka karar da lauya mai kare Wanda ke kara ta shigar, bisa rashin cika ka’idoji shigar da karar a kotun daukaka karar ta tarayya dake Kaduna, sannan ta nemi ya biya tarar naira dubu dari biyu ga masu karar kamar yadda lauyan mai kare wanda ake karar ya nema.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Da yake karin bayani game da wannan Zama lauyan wanda ake kara, Mista Abdullahi Yahya SAN, ya ce, da wannan korar karar da aka yi, ya Basu damar Cigaba da aiki da wancan hukuncin da kotun bayan ta yanke na yin gwanjon wasu daga cikin kadarorin Hon. Mahmood Sani Sha’aban don biyan bashin da Alhaji Umar Faruk Abdullahi ke binsa.

A nata bangaren lauyan mai kara, Halima Fumilola Olodo, ta tabbatar da cewa rashin cika wasu daga cikin ka’idojin shigar da karar a kotun daukaka karar ya sa aka kori karar.

Ita dai wannan shari’ar ta samo asali ne daga wata yarjejeniyar bashi da aka sanya wa hannu a shekarar 2018 tsakanin Hon. Sani Mahmood Sha’aban (Dan Buran Zazzau) da Alhaji Umar Faruk Abdullahi domin taimaka wa Sha’aban ya samu ‘yanci daga matsalar kama shi da tsare shi da akayi a gidan yari a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), a wancan shekarar.

An ba Sha’aban bashin dala miliyan ɗaya na Amurka ($1,000,000) da kuma naira miliyan 11.2 ba tare da riba ko ruwa ba, bisa tanade-tanaden shari’ar Musulunci, tare da sharadin cewa zai mayar da bashin cikin watanni shida.

Lauyoyin Sha’aban ne suka tsara tare da shaida yarjejeniyar, sannan ɗansa ya sanya hannu a madadinsa kafin daga bisani, bayan dawowarsa daga gidan yari, shi ma ya sanya hannu domin amincewa da ita.

Sha’aban ya riga ya fara biyan chabar kudi har dala $290,762 daga cikin bashin dala miliyan ɗaya, amma daga baya ya ƙi biyan ragowar bashin. Daya daga cikin sharuɗɗan yarjejeniyar ita ce a biya bashin cikin watanni shida tare da mayar da shi da irin kuɗin da aka karɓa da su.

Kotu
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
  • Sulaiman
    Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
  • Sulaiman
    Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
  • Sulaiman
    Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

June 18, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.