• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kare hakkin bil’Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana ganin Isra’ila na ci gaba da saba dokokin duniya a ruwan bama-bamai da take yi a Gaza.

Hukumar ta yi nazari a kan wasu hare-haren bam shida da Isra’ilar ta kai a shekarar da ta wuce, wadanda ta kai gidajen jama’a da makaranta da sansanonin an gudun hijira da kuma wata kasuwa.

  • Muhimmiyar Takarda Kan Yanke Hukunci Mai Tsanani Kan Masu Yunkurin Balle Taiwan Daga Kasar Sin Ta Bullo Da Wasu Sakwanni Uku
  • Firaministan Kasar Kyrgyzstan: Layin Dogon Da Ya Hada Kasashen Sin Da Kyrgyzstan Da Uzbekistan Zai Taimaka Ga Raya Kyrgyzstan Har Ta Zama Mahadar Jigilar Hajoji

Ta ce, manyan makaman da aka yi amfani da su ba za su iya tantance tsakanin farar hula da mayaka ba, saboda haka babu dalilin yin amfani da su a wuraren.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta tabbatar da mutuwar mutum 218 a hare-haren amma tana ganin yawan ma ya fi haka.

Babban Jami’in Kula da Hakkin Dan’Adam na Majalisar, Bolker Turk, ya ce hare-haren bom na Isra’ila ka iya zama laifukan cin zarafin bil’Adama.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Al’ummar Zirin Gaza na cikin mawuyacin hali na mummunar illa ga lafiya da kuma muhallinsu saboda yakin da Isra’ila ke yi da Hamas ya tilasta musu zama cikin kazanta.

Asmahan al-Masri, wacce ta yi gudun hijira daga Beit Hanoun, yanzu tana zaune a Khan Younis, ta bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan mummuke, inda ta koka da cututtukan da jikokinta ke fama da su, wadanda suka hada da karzuwa.

A cikin wata takwas da ya gabata, fiye da tan 330,400 na bola aka tara a Gaza, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin agaji suka bayyana.

Mutum 16 na dangin Masri na cunkushe a cikin wani tanti kusa da jami’ar al-Aksa, kewaye da kudaje da karnuka da warin sharar da ta rube.

Mawuyacin hali ya tilasta wa mutane da yawa, kamar Mohamed, kalen abinci da sauran tarkace domin sayarwa don su rayu.

Sama da mutum miliyan daya da suka tsere daga harin da sojojin Isra’ila suka kai a Rafah yanzu haka suna zaune a yankunan da suka koma wurin tara shara na wucin-gadi.

Ali Nasser, wanda kwanan nan ya koma sansanin jami’ar al-Aksa daga Rafah, ya bayyana irin halin da suke ciki da suka hada da larurar amai da gudawa, da kuma karzuwa saboda rashin kyawun rayuwa.

Shekaru da dama da Isra’ila da Masar suka yi na killace yankin ya haifar da cikas ga ayyukan yau da kullum kamar zubar da shara a Gaza.

Tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, sojojin Isra’ila suka toshe hanyoyin shiga manyan wuraren da ake zubar da shara a Gaza, lamarin da ya ta’azzara rikicin.

A cewar Sam Rose, darektan tsare-tsare na hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA, yanayin kula da shara a Gaza ya tabarbare matuka.

Hotunan shafukan intanet da binciken da BBC Berify ta yi sun nuna yadda ake samun yawan zubar da shara barkatai, yayin da mutane ke tserewa zuwa garuruwa da birane daban-daban.

Yawancin wuraren kula da ruwa da bahaya sun lalace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaIsra'ilaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Kasar Zimbabwe Ya Aure Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki

Next Post

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Related

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

38 minutes ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

4 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

5 days ago
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
Kasashen Ketare

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

7 days ago
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Kasashen Ketare

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

1 week ago
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

1 week ago
Next Post
Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallamii Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallamii Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.