• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kare hakkin bil’Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana ganin Isra’ila na ci gaba da saba dokokin duniya a ruwan bama-bamai da take yi a Gaza.

Hukumar ta yi nazari a kan wasu hare-haren bam shida da Isra’ilar ta kai a shekarar da ta wuce, wadanda ta kai gidajen jama’a da makaranta da sansanonin an gudun hijira da kuma wata kasuwa.

  • Muhimmiyar Takarda Kan Yanke Hukunci Mai Tsanani Kan Masu Yunkurin Balle Taiwan Daga Kasar Sin Ta Bullo Da Wasu Sakwanni Uku
  • Firaministan Kasar Kyrgyzstan: Layin Dogon Da Ya Hada Kasashen Sin Da Kyrgyzstan Da Uzbekistan Zai Taimaka Ga Raya Kyrgyzstan Har Ta Zama Mahadar Jigilar Hajoji

Ta ce, manyan makaman da aka yi amfani da su ba za su iya tantance tsakanin farar hula da mayaka ba, saboda haka babu dalilin yin amfani da su a wuraren.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta tabbatar da mutuwar mutum 218 a hare-haren amma tana ganin yawan ma ya fi haka.

Babban Jami’in Kula da Hakkin Dan’Adam na Majalisar, Bolker Turk, ya ce hare-haren bom na Isra’ila ka iya zama laifukan cin zarafin bil’Adama.

Labarai Masu Nasaba

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Al’ummar Zirin Gaza na cikin mawuyacin hali na mummunar illa ga lafiya da kuma muhallinsu saboda yakin da Isra’ila ke yi da Hamas ya tilasta musu zama cikin kazanta.

Asmahan al-Masri, wacce ta yi gudun hijira daga Beit Hanoun, yanzu tana zaune a Khan Younis, ta bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan mummuke, inda ta koka da cututtukan da jikokinta ke fama da su, wadanda suka hada da karzuwa.

A cikin wata takwas da ya gabata, fiye da tan 330,400 na bola aka tara a Gaza, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin agaji suka bayyana.

Mutum 16 na dangin Masri na cunkushe a cikin wani tanti kusa da jami’ar al-Aksa, kewaye da kudaje da karnuka da warin sharar da ta rube.

Mawuyacin hali ya tilasta wa mutane da yawa, kamar Mohamed, kalen abinci da sauran tarkace domin sayarwa don su rayu.

Sama da mutum miliyan daya da suka tsere daga harin da sojojin Isra’ila suka kai a Rafah yanzu haka suna zaune a yankunan da suka koma wurin tara shara na wucin-gadi.

Ali Nasser, wanda kwanan nan ya koma sansanin jami’ar al-Aksa daga Rafah, ya bayyana irin halin da suke ciki da suka hada da larurar amai da gudawa, da kuma karzuwa saboda rashin kyawun rayuwa.

Shekaru da dama da Isra’ila da Masar suka yi na killace yankin ya haifar da cikas ga ayyukan yau da kullum kamar zubar da shara a Gaza.

Tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, sojojin Isra’ila suka toshe hanyoyin shiga manyan wuraren da ake zubar da shara a Gaza, lamarin da ya ta’azzara rikicin.

A cewar Sam Rose, darektan tsare-tsare na hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA, yanayin kula da shara a Gaza ya tabarbare matuka.

Hotunan shafukan intanet da binciken da BBC Berify ta yi sun nuna yadda ake samun yawan zubar da shara barkatai, yayin da mutane ke tserewa zuwa garuruwa da birane daban-daban.

Yawancin wuraren kula da ruwa da bahaya sun lalace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaIsra'ilaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Kasar Zimbabwe Ya Aure Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki

Next Post

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Related

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
Kasashen Ketare

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

2 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

1 week ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

2 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

3 weeks ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

3 weeks ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

3 weeks ago
Next Post
Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.