Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin dakatar da sare bishiyoyi ba bisa ka’ida ba a harabar gidan talabijin mallakin jihar, Abubakar Rimi Television, bayan wani bidiyo da ya nuna yadda ake sare bishiyoyi a wurin ya karaɗe shafukan sada zumunta.
Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayar da umarnin yayin wata ziyarar ba zata da ya kai gidan talabijin din a ranar Asabar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar yada labarai da harkokin cikin gida ta jihar Kano, Ameen Yassar, ya fitar ranar Asabar.
Waiya ya ce wannan ɗabi’a ta saɓa wa manufofin gwamnatin jihar na kare muhalli da yaki da sauyin yanayi, yana mai gargaɗin cewa duk wani yunƙuri na sake sare bishiyoyi a harabar gidan talabijin din dole ne ya samu amincewar hukumomi bayan tuntuɓar hukumomin gwamnati da abin ya shafa.Ya nuna damuwa kan lamarin, yana mai cewa lalacewar albarkatun kasa na haifar da mummunan tasiri ga muhalli.














Discussion about this post