Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya bukaci Rundunar ‘Yansanda da ta hada kai da sarakunan gargajiya domin magance matsalolin tsaro da ke addabar al’umma a Sakkwato.
Sarkin Musulmi ya bayyana hakan ne a yayin da ya karbi bakuncin sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Sakkwato, Hayatu Hassan Shafa a ziyarar girmamawa da ya kai a fadarsa domin gabatar da kansa a hukumance.
A jawabinsa Sarkin Musulmi ya ce amfani da hanyoyin tattara bayanan sirri da kuma kusancin da sarakunan gargajiya ke da shi da al’umma a matakin kasa na da matukar muhimmanci wajen magance matsalolin tsaro a Sakkwato da kasa bakidaya.
Ya ce sarakunan gargajiya sun fi kusa da jama’a, sun san yankuna, iyalai da kuma zirga-zirgar al’umma, don haka hada guiwar aiki da su kafada da kafada zai taimaka wajen tattara sahihan bayanan da za su taimaka wajen tabbatar da sha’anin tsaro a Sakkwato.
Kwamishinan ya tabbatarwa Sarkin Musulmi da kudurinsa lna kulla kyakkyawar alaka tsakanin rundunar ‘yan sanda da sarakunan gargajiya.
Ya ce gudunmuwar da sarakuna ke bayarwa wajen wanzar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin al’umma ba karama ba ce wadda ‘yan sanda za su ci-gaba da nasu kokarin domin samar da tsaro a cikin al’umma.














Discussion about this post