Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun saki mata da yara 416 da aka sace daga al’ummar Ngoshe da ke karamar hukumar Gwoza a jihar Borno, lamarin da ya kawo sauki ga iyalan wadanda aka sace bayan kusan kwashe makonni 12 da faruwar lamarin.
Shugaban kungiyar matasan Borno ta Kudu (BOSYA), Samaila Kaigama, ne ya tabbatar da hakan ranar Lahadi, yana mai cewa wadanda aka sace sun samu ’yanci ne ranar Asabar, 6 ga Yuni, bayan ci gaba da tattaunawa da kokarin shiga tsakani da kungiyar ta yi.
A cewar Kaigama, kungiyar BOSYA ta ci gaba da shiga tsakani tsakanin ’yan ta’addan da wadanda abin ya shafa tun bayan da kungiyar Boko Haram ta fara nuna mutanen da ta sace a watan Afrilu.
Ya ce, “BOSYA ta samu nasarar kubutar da dukkan mata da yara 416 na Ngoshe. An sake su ne a ranar 6 ga Yuni.”














Discussion about this post