An gudanar da wani taron tattaunawa mai taken “Tides and Voices”, wanda cibiyar shirye-shirye ta harshen Sinanci ta babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG ta dauki nauyin shiryawa, a reshen CMG da ke birnin Sanya a jiya Jumma’a. Taron ya hada masana na Sin da na kasashen waje daga kwamitin masana masu nazarin harkokin tekun kudancin Sin na CMG, inda suka yi tattaunawa mai zurfi kan batutuwan da suka shafi tekun kudancin Sin kamar tafiyar da harkokinsa, da hadin gwiwa, da tsaron yankin.
Masanan da suka halarci taron sun amince cewa duk da cewa yanayin tekun kudancin Sin na cikin kwanciyar hankali, tsoma baki daga waje shi ne babban abin da ke kara barazanar tsaron yankin.
Jerin mummunan ayyukan da wasu sojojin waje ke yi, da kuma hadin gwiwarsu da Philippines, sun kawo cikas ga tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu, wanda ke bukatar taka tsantsan daga kasashen yankin.(Safiyah Ma)















Discussion about this post