ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
55 minutes ago
Kaduna

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na sa-kai sun dakile yunkurin satar shanu da garkuwa da mutane guda biyu a kananan hukumomin Igabi da Kudan na jihar, inda suka ceto jimillar shanu 245 da aka sace.

Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da wadannan ayyuka ne a ranar 31 ga Mayu bayan hadin gwiwar jami’an ‘yan sanda, masu tsaron sa-kai da kuma al’umma.

A wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar ranar Litinin, ya ce da sanyin safiyar Lahadi wasu ‘yan bindiga sun kai hari wani matsugunin Fulani da ke wajen kauyen Rubu a Karamar Hukumar Igabi, inda suka daure makiyaya uku da wasu masu gadi kafin su tafi da shanu masu yawa.

ADVERTISEMENT

Hassan ya ce shugaban kungiyar Miyetti Allah a Karamar Hukumar Igabi ne ya kai rahoton lamarin, wanda hakan ya sa jami’in ‘yansanda na Rigachikun Dibision ya tattara jami’ansa tare da masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah da kuma mambobin Cibilian Joint Task Force domin gudanar da aikin ceto.

“Kungiyar hadin gwiwar ta bi sawun wadanda ake zargi tare da sanar da al’ummomin da ke makwabtaka da wurin da kuma matsa musu lamba sosai.

LABARAI MASU NASABA

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

“Saboda tsananin matsin lambar da aka musu, ‘yan bindigar sun yi watsi da shanun da suka sace da kuma mutanen da suka kama, sannan suka tsere zuwa cikin daji. An ceto fiye da shanu 200 cikin koshin lafiya, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke wadanda suka tsere,” in ji sanarwar.

A wani lamari makamancin haka, rundunar ta ce an sake ceto wasu shanu 45 a wani samame da aka kai a Hunkuyi.

Rundunar ta bayyana cewa bayan samun rahoton satar shanu, jami’in ‘yansanda na Hunkuyi Dibision ya kaddamar da bincike da sintiri, wanda ya haifar da samun sahihan bayanan sirri cewa an boye shanun da aka sace a cikin wani daji da ke Hawan Mai Mashi a kan hanyar Zariya zuwa Kano.

Sanarwar ta ce an tura hadaddiyar tawaga ta jami’an ‘yansanda da ma’aikatan Jihar Kaduna Bigilance Serbice zuwa yankin.

“Da ganin jami’an tsaron, ‘yan bindigar masu dauke da makamai sun bude musu wuta. Jami’an tsaron sun mayar da martani da karfin wuta mafi karfi, lamarin da ya tilasta wa ‘yan bindigar tserewa da raunukan harbin bindiga, tare da barin dukkan shanun 45,” in ji Hassan.

Kakakin rundunar ya kara da cewa ana ci gaba da bincike domin cafke wadanda suka tsere da kuma rusa kungiyar masu aikata wadannan laifuka.

Ya kuma bayyana cewa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin ‘yansanda, masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah, Cibilian Joint Task Force, Kaduna State Bigilance Serbice da kuma al’umma, yana mai cewa nasarar ayyukan ta nuna tasirin amfani da bayanan sirri da kuma tsarin tsaro na hadin gwiwa da al’umma.

Muhammad ya bukaci mazauna jihar su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai cikin lokaci domin taimakawa yaki da ayyukan ta’addanci da sauran laifuka a fadin jihar.

Ya kuma jaddada aniyar rundunar na kare rayuka, dukiyoyi da dabbobi a dukkan sassan Jihar Kaduna.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Kotu Da Ɗansanda

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
Next Post
Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

June 6, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai

Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai

June 6, 2026
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

June 6, 2026
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.