ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Kaduna

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na sa-kai sun dakile yunkurin satar shanu da garkuwa da mutane guda biyu a kananan hukumomin Igabi da Kudan na jihar, inda suka ceto jimillar shanu 245 da aka sace.

Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da wadannan ayyuka ne a ranar 31 ga Mayu bayan hadin gwiwar jami’an ‘yan sanda, masu tsaron sa-kai da kuma al’umma.

A wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar ranar Litinin, ya ce da sanyin safiyar Lahadi wasu ‘yan bindiga sun kai hari wani matsugunin Fulani da ke wajen kauyen Rubu a Karamar Hukumar Igabi, inda suka daure makiyaya uku da wasu masu gadi kafin su tafi da shanu masu yawa.

ADVERTISEMENT

Hassan ya ce shugaban kungiyar Miyetti Allah a Karamar Hukumar Igabi ne ya kai rahoton lamarin, wanda hakan ya sa jami’in ‘yansanda na Rigachikun Dibision ya tattara jami’ansa tare da masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah da kuma mambobin Cibilian Joint Task Force domin gudanar da aikin ceto.

“Kungiyar hadin gwiwar ta bi sawun wadanda ake zargi tare da sanar da al’ummomin da ke makwabtaka da wurin da kuma matsa musu lamba sosai.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Saboda tsananin matsin lambar da aka musu, ‘yan bindigar sun yi watsi da shanun da suka sace da kuma mutanen da suka kama, sannan suka tsere zuwa cikin daji. An ceto fiye da shanu 200 cikin koshin lafiya, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke wadanda suka tsere,” in ji sanarwar.

A wani lamari makamancin haka, rundunar ta ce an sake ceto wasu shanu 45 a wani samame da aka kai a Hunkuyi.

Rundunar ta bayyana cewa bayan samun rahoton satar shanu, jami’in ‘yansanda na Hunkuyi Dibision ya kaddamar da bincike da sintiri, wanda ya haifar da samun sahihan bayanan sirri cewa an boye shanun da aka sace a cikin wani daji da ke Hawan Mai Mashi a kan hanyar Zariya zuwa Kano.

Sanarwar ta ce an tura hadaddiyar tawaga ta jami’an ‘yansanda da ma’aikatan Jihar Kaduna Bigilance Serbice zuwa yankin.

“Da ganin jami’an tsaron, ‘yan bindigar masu dauke da makamai sun bude musu wuta. Jami’an tsaron sun mayar da martani da karfin wuta mafi karfi, lamarin da ya tilasta wa ‘yan bindigar tserewa da raunukan harbin bindiga, tare da barin dukkan shanun 45,” in ji Hassan.

Kakakin rundunar ya kara da cewa ana ci gaba da bincike domin cafke wadanda suka tsere da kuma rusa kungiyar masu aikata wadannan laifuka.

Ya kuma bayyana cewa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin ‘yansanda, masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah, Cibilian Joint Task Force, Kaduna State Bigilance Serbice da kuma al’umma, yana mai cewa nasarar ayyukan ta nuna tasirin amfani da bayanan sirri da kuma tsarin tsaro na hadin gwiwa da al’umma.

Muhammad ya bukaci mazauna jihar su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai cikin lokaci domin taimakawa yaki da ayyukan ta’addanci da sauran laifuka a fadin jihar.

Ya kuma jaddada aniyar rundunar na kare rayuka, dukiyoyi da dabbobi a dukkan sassan Jihar Kaduna.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Kaduna

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.