Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na sa-kai sun dakile yunkurin satar shanu da garkuwa da mutane guda biyu a kananan hukumomin Igabi da Kudan na jihar, inda suka ceto jimillar shanu 245 da aka sace.
Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da wadannan ayyuka ne a ranar 31 ga Mayu bayan hadin gwiwar jami’an ‘yan sanda, masu tsaron sa-kai da kuma al’umma.
A wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar ranar Litinin, ya ce da sanyin safiyar Lahadi wasu ‘yan bindiga sun kai hari wani matsugunin Fulani da ke wajen kauyen Rubu a Karamar Hukumar Igabi, inda suka daure makiyaya uku da wasu masu gadi kafin su tafi da shanu masu yawa.
Hassan ya ce shugaban kungiyar Miyetti Allah a Karamar Hukumar Igabi ne ya kai rahoton lamarin, wanda hakan ya sa jami’in ‘yansanda na Rigachikun Dibision ya tattara jami’ansa tare da masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah da kuma mambobin Cibilian Joint Task Force domin gudanar da aikin ceto.
“Kungiyar hadin gwiwar ta bi sawun wadanda ake zargi tare da sanar da al’ummomin da ke makwabtaka da wurin da kuma matsa musu lamba sosai.
“Saboda tsananin matsin lambar da aka musu, ‘yan bindigar sun yi watsi da shanun da suka sace da kuma mutanen da suka kama, sannan suka tsere zuwa cikin daji. An ceto fiye da shanu 200 cikin koshin lafiya, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke wadanda suka tsere,” in ji sanarwar.
A wani lamari makamancin haka, rundunar ta ce an sake ceto wasu shanu 45 a wani samame da aka kai a Hunkuyi.
Rundunar ta bayyana cewa bayan samun rahoton satar shanu, jami’in ‘yansanda na Hunkuyi Dibision ya kaddamar da bincike da sintiri, wanda ya haifar da samun sahihan bayanan sirri cewa an boye shanun da aka sace a cikin wani daji da ke Hawan Mai Mashi a kan hanyar Zariya zuwa Kano.
Sanarwar ta ce an tura hadaddiyar tawaga ta jami’an ‘yansanda da ma’aikatan Jihar Kaduna Bigilance Serbice zuwa yankin.
“Da ganin jami’an tsaron, ‘yan bindigar masu dauke da makamai sun bude musu wuta. Jami’an tsaron sun mayar da martani da karfin wuta mafi karfi, lamarin da ya tilasta wa ‘yan bindigar tserewa da raunukan harbin bindiga, tare da barin dukkan shanun 45,” in ji Hassan.
Kakakin rundunar ya kara da cewa ana ci gaba da bincike domin cafke wadanda suka tsere da kuma rusa kungiyar masu aikata wadannan laifuka.
Ya kuma bayyana cewa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin ‘yansanda, masu tsaron sa-kai na Miyetti Allah, Cibilian Joint Task Force, Kaduna State Bigilance Serbice da kuma al’umma, yana mai cewa nasarar ayyukan ta nuna tasirin amfani da bayanan sirri da kuma tsarin tsaro na hadin gwiwa da al’umma.
Muhammad ya bukaci mazauna jihar su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai cikin lokaci domin taimakawa yaki da ayyukan ta’addanci da sauran laifuka a fadin jihar.
Ya kuma jaddada aniyar rundunar na kare rayuka, dukiyoyi da dabbobi a dukkan sassan Jihar Kaduna.















Discussion about this post