ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
33 minutes ago
Nijeriya

An yanke wa wasu maza biyu hukuncin daurin shekaru 24 da watanni biyar gaba daya saboda rawar da suka taka a wani mummunan hadarin mota da ya yi sanadin mutuwar wani dan Nijeriya mazaunin Birtaniya, Sylbester Abayomi, a birnin Manchester.

Wadanda aka samu da laifin, Uways Hussain mai shekaru 20 da Usmon Mahmood mai shekaru 23, an yanke musu hukunci bayan an same su da laifi kan hadarin da ya faru a watan Maris na shekarar 2026 a titin Kingsway da ke Manchester, wanda ya yi sanadin mutuwar Abayomi.

Rahotanni sun nuna cewa Hussain ya samu hukuncin daurin shekaru 11 da watanni takwas, yayin da Mahmood ya samu shekaru 12 da watanni tara a gidan yari.

ADVERTISEMENT

Sanarwar da ‘yansandan Greater Manchester suka fitar ta bayyana cewa hukuncin Mahmood na daga cikin na farko a Birtaniya inda aka samu wani fasinja da laifin taimakawa da karfafa aikata laifin haddasa mutuwa ta hanyar tuki cikin hadari.

Binciken ‘yansanda ya nuna cewa mutanen biyu sun kwashe daren kafin hadarin suna yawo a Kudancin Manchester cikin ganganci da gudun wuce kima, tare da daukar bidiyon kansu yayin da suke tuki.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

‘Yansandan sun ce motar da aka yi hadarin da ita mallakin Mahmood ce, wanda ya ba Hussain damar tuka ta tsawon daren.

An kuma gano daga bidiyon wayoyin hannu da aka kwato cewa su biyun suna tuki da gudun da ya haura mil 100 a awa (100mph) a hanyoyin da iyakar gudu ta kasance mil 30 a awa (30mph).

Bidiyon ya kuma nuna suna karya jan fitilar hanya tare da kutsa kai tsakanin motocin da ke tafiya ba tare da la’akari da lafiyar sauran masu amfani da hanya ba.

Sanarwar ta ce: “Mutanen biyu sun kasance suna tafiya da gudun da ya wuce mil 100 a awa a hanyoyin da aka kayyade mil 30 a awa. A wasu lokuta sun kai gudun sama da mil 130 a awa, kuma dakiku kadan kafin hadarin an rubuta gudunsu ya kai mil 139 a awa.

“A wani lokaci cikin daren, sun tsaya a gidan mai inda bidiyo ya nuna Mahmood yana shakar wani iska daga cikin balan-balan yayin da yake zaune a kujerar fasinja.

“Sauran bidiyon da aka samu sun nuna Mahmood yana shakar iskar daga balan-balan yayin da Hussain ke tuki da gudun sama da mil 100 a awa, inda shi ma Hussain ya bayyana yana yin hakan.”

‘Yansandan sun ce hadarin ya faru da misalin karfe 4:36 na asubahin watan Maris 2026 a mahadar titunan Green End Road da Kingsway.

Marigayin Abayomi na kan hanyarsa ta zuwa aiki ne, kuma ya shiga mahadar ne bayan ya samu koren hasken hanya, yana tunanin yana da lafiya ya wuce. Sai dai wata mota kirar Bolkswagen Golf da Hussain ke tuka wa, wadda ta karya jan fitila cikin matsanancin gudu, ta bugi motarsa.

“Sylbester yana kan hanyarsa ta zuwa aiki kuma ya shiga mahadar ne da koren haske, yana ganin hanya lafiya ce. Daga nan ne motar Bolkswagen Golf da Hussain ke tuka wa ta buge shi bayan ta karya jar fitila cikin tsananin gudu,” in ji ‘yansandan.

Jami’an agajin gaggawa sun garzaya wurin hadarin, amma Abayomi ya rasu sakamakon munanan raunukan da ya samu.

Sanarwar ta kara da cewa bayan hadarin, mutanen biyun sun fara tattauna yadda za su tsere da kuma yadda za su boye wasu hujjoji.

Wani sakon gaggawa da agogon Apple Watch na Hussain ya aika kai tsaye bayan hadarin ya dauki hirarsu, inda aka ji suna tattauna yadda za su gudu daga wurin da kuma irin hujjojin da ya kamata su cire daga motar.

An kuma ji suna tattauna yiwuwar kai rahoton cewa an sace motar. Daga bisani, sun yi odar motar Uber domin tserewa daga wurin.

‘Yansandan Greater Manchester sun ce sun samu rahoton farko da karfe 4:37 na asubahin, kuma cikin mintuna 12 kacal jami’ansu sun gano inda mutanen biyu suke tare da kama su.

Bayanan da aka ciro daga motar Bolkswagen Golf sun tabbatar da cewa motar ta kai gudun mil 139 a awa a dakikun da suka gabaci mummunan hadarin da ya yi sanadin mutuwar Abayomi.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

MASU ALAKA

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

June 6, 2026
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.