ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ISWAP Ta Kashe ‘Yan Gudun Hijira 35 A Jihar Borno 

by Sadiq
3 years ago
ISWAP

Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 35 ’yan gudun hijira da suka je yin su a yankin Mukdolo da ke Karamar Hukumar Ngala ta Jihar Borno.

Wani masunci da ya tsallake rijiya da baya ya shaida wa Aminiya cewa a ranar Laraba ne mayakan na ISWAP sun ritsa su ne ta gabar kogi, suka bude musu wuta inda mutum 35 suka mutu, wasu da dama kuma ba a san inda suka shige ba.

  • Zaben Gwamnoni: Kotu Ta Bai Wa INEC Umarnin Amfani Da Katin Zabe Na Wucin Gadi
  • Taruka 2 Na Kasar Sin: A Kara Fahimtar Cikakken Tsarin Demokuradiyya Da Ake Damawa Da Jama’a

Ya ce “Sun bullo ne daga cikin kungurmin daji a kan babura, suka zagaye mu ta gabar kogin, cewa ‘mun sha jan kunnenku cewa ku daina zuwa nan, amma sai kuka rika gaya wa sojoji inda muke.

ADVERTISEMENT

“Daga nan suka fara harbi ta kowace kusurwa, mutum uku kacal suka koma Dikwa da ransu, amma ina tabbatar da cewa mutum sama da 35 aka kashe; yanzu haka mutane da yawa ba su dawo garin Dikwa ba.”

Ya ce lamarin ya faru ne a kauyen Mukdolo da ke kusa da garin Dikwa kuma daukacin ’yan gudun hijirar sun fito ne daga Dikwa.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Da yake tabbatar da labarin harin, Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da tayar da kayar baya da kuma sharhi kan sha’anin tsaro a yakin Tabkin Chadi, ya ce an gano gawar mutum 26 daga cikin ’yan gudun hijirar da kungiyar ta kashe.

 

Ya ce mutum tara daga cikin masuntan da aka kai wa hari sun tsira, amma uku daga cikinsu sun samu raunukan harbi.

Ya bayyana cewa sai da mayakan “Suka sa mutanen kwantawa, suka daddaure su da ragar kamun kifi, sannan suka har suka galabaita, sannan suka bude musu wuta.

“Sojoji sun gano gawarwakin mutum 26 a cikin daji bayan da suka samu labarin abin da ya faru daga sauran wadanda suka tsare,” in ji shi.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayar Kasarsa Kan Takunkuman Sudan

Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayar Kasarsa Kan Takunkuman Sudan

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.