Iyayen Jinkai Simon mai shekaru 17 ‘yar asalin Jihar Filato, sun zargi Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da musuluntar da ‘yarsu tare da aurar da ita bayan ta ɓace a Jihar Kaduna.
A cewar wata takarda da suka aike wa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kaduna a ranar 6 ga watan Mayu, iyalan sun ce Jinkai, wadda ke karatu a makarantar St. Bartholomew’s da ke Wusasa a Zariya, ta ɓace ne ranar 9 ga watan Maris bayan ta tafi makaranta.
Iyayen sun ce gani na ƙarshe da aka mata shi tare da wata maƙwabciyarsu mai suna Ruqaiya, wadda daga baya ta sanar da su cewa Jinkai ta musulunta kuma an kai ta Kano.
Sun zargi Hisbah da ta canja mata sunanl daga Jinkai Simon zuwa Aisha Sani kafin daga baya suka aurar da ita ga wani mutum mai suna Abdulsamad.
Iyayen sun kuma zargi hukumar da canja shekarunta daga 17 zuwa 19 a wasu takardu da suka nuna cewar iyayenta ne suka sanya wa hannu.
A cewar takardar ƙorafin, an kai Jinkai wata babbar kotun Jihar Kano inda aka sa ta rantse cewa shekarunta 19.
Iyayen sun buƙaci ‘yansanda su binciki lamarin tare da tabbatar da dawo da ‘yarsu gida lafiya.
An kuma aike kwafin takardar zuwa ofishin Sufeto Janar na ‘Yansanda, Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya, reshen Jihar Kaduna, Anglican Diocese na Wusasa da wasu ƙungiyoyin Kirista.
A lokacin haɗa wannan rahoto, Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ba ta fitar da wata sanarwa kan zarge-zargen ba.















Discussion about this post