Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce jam’iyyar NDC da ADC za su iya haɗa kai kafin zaɓen shekarar 2027.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise.
Hakazalika ya yi magana kan ficewarsa daga ADC da kuma haɗin gwiwarsa da Peter Obi.
A cewarsa, sauye-sauye da dama na faruwa a siyasar Nijeriya, amma manyan ‘yan siyasa sun mayar da hankali kan addini da ƙabilanci.
Ya ce matasa a Nijeriya sun fi mayar da hankali kan shugabanci na gari da zai iya magance matsalolin ƙasa.
Kwankwaso ya ƙara da cewa wannan hangen nesa na matasa ya fi dacewa domin ci gaban Nijeriya.
Masana harkokin siyasa na ganin irin sauye-sauyen da ake samu a baya-bayan za su yi tasiri a siyasar 2027 da ke ƙara tunkarowa.















Discussion about this post