• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jabun Kayayyaki Sun Mamaye Kasuwannin Nijeriya

by Ra'ayinmu
6 months ago
in Labarai
0
Jabun Kayayyaki Sun Mamaye Kasuwannin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba karamar damuwa ce, musamman ma ga masu kishin Nijeriya,idan aka yi la’akari da sanarwar da hukumar  kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta yi na cewar, ta lalata jabun Magununa da kudinsu ya kai  sama da Naira biliyan 120, a cikin watannin shida da suka gabata kacal.

Wannan adadin, ya kai na yawan jabun magungunan da Hukumar ta kwace ne daga watannin Oktoba zuwa Disamba na 2024.

  • Fashewar Bam Ya Kashe Dalibi ɗaya, Ya Jikkata 4 Abuja
  • Sukar Gwamnatin Tinubu: Haƙiƙanin Gaskiyar Kama Obi A Abuja

Adadin, ya jefa matukar fargaba a zukatan al’ummar kasa da ke yin amfani da magungunan wajen nemawa kansu lafiya, musamman ma  irin wannan dimbin magungunan na jabun da ake shigowa da su cikin Nijeriya, aka kuma wucewa da su, kai tsaye, zuwa kasuwannin kasar domin sayarwa jama’a.

Hakan ya kara fallasa yadda yanayin iyakokin kasar suka kasance a matsayin kara zube wajen shigo da nau’oin jabun kaya cikin kasar, ba tare da sa idon masu kula da iyakokin kamar yadda ya kamata ba.

Kazalika ma, kwace irin wadannan jabun kayan, da bata garin masu sayar da magungunan na jabu ke yi domin samun kazamar riba, hakan na kuma kara jefa marasa lafiyar, a cikin wani mummunan yanayi na rashin lafiyar da suke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

A samamen da Hukumar ta kai a manyan Shagunan sayar da jabun magungunan da ke a kamar Legas, Fatakwal, Abiya da kuma Abuja, ta bankado irin wadannan jabun magungunan da kudinsu ya kai na sama da biliyoyin Naira.

Wannan matsalar, tana kara haifar da kalubale ga tsarin kiwon lafiyar kasar da kuma fannin tattalin arziki.

Bugu da kari, Hukumar ta kuma bankado jabun lemon Kwalba a wajen baje kolin kaya da ke  jihar Legas, tare da kuma  garkame wasu masana’antun da suke sarrafa Shinkafar da ta lalace da kudinta ya kai kimanin Naira biliyan biyar a jihar Nasarawa, wanda hakan ya nuna irin babbar ta’asar da masu son kazamar ribar, suke aikatawa.

Wannan gano jabun kayan, ya zo daidai da lokacin da ake yin nazari kan yawan kudaden da marasa lafiya suka kashe, wajen sayen magunguna.

Shugabar Hukumar ta kasa Farfesa Mojisola Adeyeye ta alakanta irin wadannan masu sayar da jabun magungunan domin samun kazamar riba, a matsayin makasa.

Hukumar ta kuma kulle manyan Shaguna 150 a kasuwar Eziukwu, da ke a yankin Aba da ake sayar da jabun Lemon Kwalba.

Kazalika ma, sayar da irin wannan jabun kayan yana hanawa Gwamnati samun kudaden shiga, tare da kuma da zubar da mutuncin Nijeriya, a idon kasuwar duniya, inda kuma a yayin da irin wadannan jabun magungunan suka cike kasuwa, ke haifar da gasa a tsakanin ainihin masu sarrafa magungunan na gaske, tare da haifar masu da asara da durkushewar kasuwancinsu.

Bisa ga namu ra’ayin, a yayin da hukumar NAFDAC ke kara jajircewa wajen yakar irin wadancan mutanen masu sarrafa jabun magungunan, ta canci yabo.

Yadda aka lalata jabun kayan da kudinsu su ka kai na kimanin Naira biliyan 120, hakan ya nuna cewa, akwai gazawa ta magance matsalar.

Kazalika, hakan ya janyo bijero da tambaya a zukatan ‘yan Nijeriya, na rashin sa ido a iyakokin kasar.

Ya zama wajibi ne a dauki matakai daban daban domin kawo karshen ita wannan matsalar.

daya daga cikin matakan, na farko, ya kamata a kulla hadaka mai karfi a tsakanin NAFDAC da jami’an Hukumar Kwastam da kuma sauran Hukumomin tsaro, don a dakile shigo da jabun kaya cikin kasar.

Abu na biyu kuma shi ne, a rinka hukunta su batagarin da suke sarrafa kayan jabun, don hakan ya zama darasi ga sauran masu tunanin aikata  irin haka a nan gaba.

Kuma ya kamata a rinka yin amfani da kimiyyar zamani wajen dakile shigo da kayan na jabu da kuma samar da na’urorin zamani, da za su rinka tantance, kayan da ake shigowa da su.

Kazalika ma, ya zama wajbi, Hukumar NAFDAC, ta kara kaimi wajen ilimantarwa da fadakar da ‘yan kasar kan sayen kaya masu inganci,don  haka akwai bukatar a samar da shirye-shiyen ilmantarwa a makarantu da hakanan  a cikin al’umomi, kan yadda za a iya saurin gane jabun kaya a kuma  kai rahoto, ga mahukuntan kasar nan.

Akwai matukar bukatar sahihan kamfanoni masu zaman kansu da masu saye da sayarwa, suma su kara jan damara, wajen yakar masu sarrafa kayan jabu, musamman ma ta hanyar yin amfani da kimiyyar zamani, don gano jabun kaya.

Ya kuma kamata su rika yin aiki kafada – kafada da Hukumomi a kasar nan, domin kare kayan da suke sarrafawa da kuma kare lafiyar, masu sayen kayan domin su yi amfani da su.

Idan har ba a kawo karshen wadannan matsalolin da aka zayyana a sama ba, za ci gaba da komawa ‘yar gidan jiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwa Da Ɗanta Sun Ƙone Ƙurmus A Wata Gobara Abuja

Next Post

Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

9 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

12 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

13 hours ago
Next Post
Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare

Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.