ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Gusau Ta Kori Dalibai 7 Ta Dakatar Da Karatun 6 Kan Rashin Da’a

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jami'ar Gusau

Jami’ar Gwamnatin tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara ta dauki mataki mai tsauri na ladabtar da dalibai 13 ciki har da mata uku da aka samu da laifuka daban-daban da suka kunshi sata, coge don samun damar karatu, satar jarabawa da sauransu.

 

A sanarwar manema labarai da jami’in watsa labarai na jami’ar Malam Umar Usman ya fitar, ya ce, laifukan da aka samu daliban da aikatawa sun saba wa sashin doka A item (xxv) shafi na 62, da shafi 68 item (iv) na kundin tsare-tsare da dokokin da ke tafiyar da da’ar dalibai, tare da sashi L shafi 69-73 item (i-xxv) na kundin littafin dalibai.

ADVERTISEMENT
  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Sayar Da Hannun Jarin Wasu Tashoshin Jiragen Sama

Ya ce: “Hukumar gudanarwar jami’ar a zamanta karo na 82 da ya gudana a ranar 5 ga watan Yulin 2023 ta yi nazari da la’akari da shawarorin da rahoton kwamitin ladabtar da dalibai (SDC) ya bayar na kokar dalibai bakwai da dakatarwa/tsawaita wa’adin karatun dalibai 6 bisa samun su da laifukan rashin da’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

“Daliban da lamarin ya shafa sun aikata laifukan da suka saba wa dokokin da ke tafiyar da harkokin dalibai na jami’ar,” ya shaida.

 

Ya kuma ce dauka da tabbatar da wannan matakin ya fito ne daga wajen mai rikon sakataren ilimi na jami’ar, Malam Mu’awiyya Bello a madadin rijista Malam Yakubu Audu Anivbassa da ya fitar a ranar 7 ga Yuli.

 

Daliban da wannan matakin na korar ya shafa sun hada da Daniel Ibeh Mayowa, Habibu Abdul, Abdulsalam Abubakar, Faruk Alayande Olamilekam, Iortim Philemon Vasue, Abubakar M. Usman tare da James Joseph.

 

Sannan wadanda kuma aka Dakatar da karatunsu na wasu lokuta daga zangon karatu daya wasu zangon karatu biyu; Emmanuel Chibuzor Ejikeme, Idowu Ojo Oni, Khadija Abdulrahman Bala, Sadiya Sani Garba, Balkisu Bello da kuma Ibrahim Mu’azu Lawal.

Jami'ar Gusau
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Labarai

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Next Post
NATO Har Tana Son Sa Hannu Cikin Harkokin Yankin Asiya Da Pasifik

NATO Har Tana Son Sa Hannu Cikin Harkokin Yankin Asiya Da Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.