ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Kano Ta Rantsar Da Dalibai 1,200 A Zangon Karatu Na 2022/23

by Bello Hamza
3 years ago
Kano

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

  • PLA Za Ta Gudanar Da Sintirin Gargadi A Kewayen Tsibirin Taiwan
  • Buhari Ya Yi Kira A Kawo Karshen Kashe-Kashe A Benue

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Kano
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Gwamnatin Kaduna Ta Dage Dokar Hana Fita A Chikun

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.