• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Kano Ta Rantsar Da Dalibai 1,200 A Zangon Karatu Na 2022/23

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Jami’ar MAAUN Kano Ta Rantsar Da Dalibai 1,200 A Zangon Karatu Na 2022/23
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

  • PLA Za Ta Gudanar Da Sintirin Gargadi A Kewayen Tsibirin Taiwan
  • Buhari Ya Yi Kira A Kawo Karshen Kashe-Kashe A Benue

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaikanoMAAUN
ShareTweetSendShare
Previous Post

PLA Za Ta Gudanar Da Sintirin Gargadi A Kewayen Tsibirin Taiwan

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Dage Dokar Hana Fita A Chikun

Related

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

30 minutes ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

2 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

3 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

4 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

5 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

6 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Gwamnatin Kaduna Ta Dage Dokar Hana Fita A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.