• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Kano Ta Rantsar Da Dalibai 1,200 A Zangon Karatu Na 2022/23

by Bello Hamza
3 years ago
Kano

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

  • PLA Za Ta Gudanar Da Sintirin Gargadi A Kewayen Tsibirin Taiwan
  • Buhari Ya Yi Kira A Kawo Karshen Kashe-Kashe A Benue

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Gwamnatin Kaduna Ta Dage Dokar Hana Fita A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.