ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Kano Ta Rantsar Da Dalibai 1,200 A Zangon Karatu Na 2022/23

by Bello Hamza
3 years ago
Kano

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

  • PLA Za Ta Gudanar Da Sintirin Gargadi A Kewayen Tsibirin Taiwan
  • Buhari Ya Yi Kira A Kawo Karshen Kashe-Kashe A Benue

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) dake Kano, ta yi nasarar rantsar da sabbin dalibai 1,200 da suka samu gurbin karatu a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a karo na biyu a ranekun Laraba 5 ga Afrilu da Alhamis 6 ga Afrilu, 2023 a tagwayen dakin taro na Farfesa Adamu Abubakar Rasheed, inda baki da aka gayyata ciki har da iyaye suka halarci taron.

An fara taron rantsarwar ne na kwanaki biyu da daliban Makarantar Kwamfuta a rana ta farko, a yayin da Makarantun Kimiyyar Zamantakewa da Gudanarwa, Kimiyyar Lafiya da Kimiyyar Jinya aka rantsar da su a rana ta biyu.

A nasa jawabin, shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa (Dr.) Mohammad Israr ya ce taron na nuni da cewa daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar an rantsar da su a hukumance kamar yadda hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta amince.

Ya taya daliban murnar samun damar shiga jami’ar sannan ya bukace su da su rungumi kyakkyawan tarbiyya tare da fuskantar karatunsu da gaske.

“Ku tuna cewa a yanzu ku jakadu ne na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya dake Kano, kuma dole ne ku bayyana a matsayin jakadu a dukkanin mu’amalarku a a cikin makarantar,” in ji Farfesa Israr.

Shugaban ya ce Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya tana gudanar da kwasa-kwasai ne kawai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwa ne da kuma dogaro da kai.

Ya gargadi daliban da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu hali na kwarai, tare da sanya tufafi na mutunci.

A nasa jawabin wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya ce nan ba da dadewa ba za a kafa makarantar kasuwanci ta MAAUN a birnin Paris domin tallafa wa dalibai a yayin da za su gudanar da bincike a karatun digirinsu na biyu da nufin mayar da takardar shaidarsu ta dace da kasashen duniya.

Ya ce ya kamata sabbin daliban su yi la’akari da cewa sun yi sa’ar samun shiga Jami’ar yana mai cewa satifiket dinsu ita ce ta fi karbuwa a Afirka ta Yamma kuma ita ce kawai takardar shaidar da ba a tantancewa a matsayin wani sharadi na samun guraben aikin yi a Amurka.

Farfesa Gwarzo ya ce daliban da suka samu gurbin karatu ya kamata su yi alfahari da kasancewarsu cikin dangin MAAUN domin za su ci gajiyar jarin da suka zuba a fannin ilimi.

Ya shaida wa daliban da aka rantsar cewa akalla dalibai 500 ne da suka kammala karatu a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer dake Maradi ke aiki a wurare daban-daban a kasar Amurka.

Ya jaddada cewa MAAUN za ta ci gaba da bayar da ilimi mai inganci domin samar da kwararrun daliban da za su bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Tun da farko, daya daga cikin ‘yan majalisar gudanarwa ta MAAUN, Farfesa Gaji Fatima Dantata, ta gabatar da sakon fatan alheri ga daliban da suka samu gurbin karatu, inda ta bukace su da su kasance masu da’a a kodayaushe domin kiyaye sunan Jami’ar da kuma cimma burinsu.

A sakon sa na fatan alheri, mataimakin shugaba, MAAUN Maradi, Dakta Shu’aibu Tanko ya taya daliban da aka rantsar da su a cikin dubban wadanda suka nemi shiga babbar jami’a.

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su dauki karatunsu da muhimmanci domin samun damar yin aiki a manyan mukamai da dama a fadin duniya bayan kammala karatunsu.

Mataimakin shugaban jami’ar bangaren gudanarwa, Dakta Habib Awais Abubakar wanda shi ne ya jagoranci gudanar da taron rantsarwa, shi ne kuma ya jagoranci rantsar da daliban.

Sauran ma’aikatan Gudanarwa da suka halarta a yayin bikin sun hada da; Mataimakin Shugaba bangaren rayuwar cikin jami’ar, Dakta Hamza Garba, Mataimakin Shugaba a bangaren sha’anin Kudi, (Dr.) Abdulrasaq Kayode, Daraktan Tsare-tsare da Tabbatar da inganci, Dakta Nura Yaro, Daraktan Cibiyar Binciken manyan Ilimi da kirkira ta Afirka, Farfesa Abubakar Sadiq Haruna.

Sauran sun hada da Daraktan hulda da hadin gwiwa, Dr. Bala Mohammed Tukur, shugaban ofishin huldar kasa da kasa, Injiniya Bashir Garba, Shugaban Makarantu, Shuwagabannin sashe, Jami’an tsaro da baki da aka gayyata da dai sauransu.

Kano
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Gwamnatin Kaduna Ta Dage Dokar Hana Fita A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.