ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Yara A Jiki Ba Tare Da Duka Ko Zagi Ba Ne Sirrin Nasarar Koyarwa—Saratu Magaji Jahun

by Bushira Nakura
4 years ago
Zagi

Saratu Magaji Usman Jahun Malamar makaranta ce wadda ta riki sana’ar koyarwar da hannu biyu-biyu, a tattunawarsu da Wakiliyarmu Bushira Nakura, ta bayyana yadda ta tsinci kanta a fagen koyarwa ta kuma yi bayanin wasu sirrorin da ke tattare da sana’ar, ta kuma yi tsokaci a kan tarihin rayuwarta. Ga dai yadda tattaunawarsu ta kasance:

Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanki da kuma sunan da aka fi saninki da shi, tare da dan takaitaccen tarihinki.

Dafar ko dai sunana Saratu Magaji Usman Jahun anfi sanina da Saratu Magaji Jahun, an haife ni a garin Jahun cikin karamar hukumar Jahun ta Jihar Jigawa, na yi karatun Firamare a Jahun, na yi Sakandire makarantar ‘yan mata ta Arabic Kaugama, na kai matakin NCE daga nan na yi aure na hayayyafa don ina da yara guda bakwai, ina jin dadin zaman aurena, Allah ya kara mana zaman lafiya mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Me ya ja hankalinki ko me ya baki sha’awa har kika zabi harkar koyarwa?

Alhamdulillah koyar wa abune mai kyau a cikin al-umma ina da ra’ayin  koyarwa tun ina kuruciya kuma har girma ya zo na tsinci kaina a harka ta koyarwa na yi farin ciki da kasan cewata malama sosai domin abin dama yana raina, Allah ya saka wa Malam mu da alkhairi,  Allah ya kara mana basira da hazaka.

LABARAI MASU NASABA

Mene Ne Ra’ayinku Kan Shigar Mata Harkokin Siyasa Gadan-gadan?

Tsakanin Yanayin Sanyi Da Na Zafi Wanne Ya Fi Maka Dadi?

Ya farkon fara koyarwar ki ta kasance wace hanya kike bi wajen shawo kan dalibanki

Kuma wacce hanya kike bi kuma ya kika tsinci kanki lokacin da kika shiga aji kasan cewar wasu na son yi amma suna jin tsoro ko kunya ke ma kin fuskanci kanki a irin wannan matsalar ko kuwa?

Da farko shiga ta aji na ji kunya gaskiya amma a hankali a hankali na saba sosai duba da irin shawarwarin da abokan aiki na suke bani  ba zan manta da Malama Halima Mukthar Jahun ba ta bani kwarin gwiywa matuka gaya Allah ya saka mata da alkhairi, sannu a hankali har na goge, na kan shiga aji zuciya ta tsab na yi koyarwata hankali kwance ina jin dadin koyarwa alal hakika gaskiya Allah ya kara mana baiwar koyar wa da hazakar shiga aji.  Na kan ji sanyi har cikin zuciya ta yayin da na shiga aji na ji yara na fadin” Malama Malama kece a jin mu” na kan yi dariya ka shiga ajin ina son dalibaina na shekarar 2004 suma suna sona sosai.

Daga lokacin da kika fara koyarwa zuwa iyanzu za ki kai kamar shekara nawa kina yi?

Na kai shekara goma sha tara ina koyarwa daga farawata zuwa yanzu da na dan samu dan canje-canje na wajen aiki.

Taya kike iya hada harkokin Gida da Aiki Masalam kula da yara kula da maigida tsaftar gida abinci da sauransu?

Wannan shi ne abu me sauki, domin tunda nasan zan fita aiki, to ya zama wajibi na tsara  fita aikina da kuma aikace aikacen gida. Ina  fara rage wasu ayyukan gidan kafin na fita, zancen Maigida da yara kuma mukam fita gaba daya sannan kusan tare muke dawowa.

Ya kike ganin yadda karbuwar ki a daga yaran da kike koyarwa?

Ita koyarwa abune da ke son jan yara a jiki, ba tare da duka ko zagi ba, Yaba wa yara lokacin da suka yi abu koda kuskure ne, daga baya sai a sanar dasu cewa hakan ba daidai ba ne, kaza ne daidai. Yara suna aso hakan.

Ta wacce hanya kike bi wajen ganin kin tankwara yaran wajen bin abinda kike so su yi?

Nakan yi abinda suke so, nima sukan yi abin da nake so.

Kowa ya san koyarwa na da wahala matuka musamman ma ta kanana yara ko me zaki ce a kan wannan?

In har ka fahimci yaran, koyar dasu ba zai ma mutum wahala ba kamar dai yadda nace jansu a jiki shi ne kaso mafi girma da malamai za su yi.

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta ga yaran ko iyayensu ko makamancin haka, me za ki ce a kan hakan?

Gaskiya ne ko wanne abu ya same ka a rayuwa sai da kalubale amma alhamdulillah ban samu kalube a cikin koyarwa da zai dameni ba saboda ‘yar kiyayya ce ta bangaren yara ai dole kasame ta duba da yanayin zamantakewa.

Wadanne irin nasarorin kika samu game da wannan sana’an naki?

Nasara Alhamdulillah, wallahi munsameta sai fatan alkhairi ba abinda zamu cewa Allah, sai godiya da fatan ya kara mana daukaka.

Shin kin taba yi a ran ki cewar dama baki zabi wannan layin na koyarwa ba ko kuwa?

Ban taba jin cewa dama ban zama Malamar makaranta ba saboda ina son koyarwa yana bani sha’awa arayuwa ta ina so na kasance Malam ta har abada Alhamdulillah.

Mene ne burinki na gaba game da wannan sana’aki?

Tofa, burina bai wucena zama shugabar makaranta (principal) ba.

Kamar wanne abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ki taba mantawa da shi ba?

Ranar da na fara karbar albashi na dubu bawai da dari duhu, na yi farin ciki ba kadan ba wallahi na yi murna na gode wa Allah subuhanahu wataala da ni’imar da ya yi min Alhamdulillah ala kullu halin.

Daga lokacin da kika fara koyar wa kawo yanzu zaki kai kamar shekara nawa?

Na kai shekara goma sha tara ina koyarwa daga farawata zuwa yanzu duk da  na dan samu dan canje-canjen a wajen aiki .

Idan kina wata sana’ar ya tsarin kasuwancin yake kasancewa, kuma ya bambancin yake kamar wajen yadda sana’ar take kawo kudi da sauransu?

Ba laifi Alhamdulillah,  sana’a tana kawo kudi, musamman idan wata ya yi nisa, ko kuma kan samu wasu suna riga wasu albashi, kinga in kana sana’a zaki samu wanda za su biyaki, kafin a samu albashi.

Wanne kira za ki yi ga matasa musamman mata wadanda ba sa sana’a ba su da abin yi, har ma da manya na gida, me za ki ce akansu?

Hakika zama ba zai yiwu babu aikinyi ba ko  kuma sana’a ba, rayuwa yanzun dole sai da neman na kai, komai kankantar sa  kuwa.

Mace da zaki gane cewa Itafa sana’a girma da daraja take karawa mutum a ko ina walau gidanki, gidanku, abokanki da duk wanda kuke tare dasu. Ya ke ‘yar uwa ki daure ki koyi sana’a kodan rufawa kanki da yaranki da iyayen ki asiri, saboda idan baki dashi ma bame nemanki.

Ko akwai wani kira da za ki ga gwamnati game da masu kokarin yin sana’a?

Mukam anan Jigawa Gwamnati na baki kokarinta a wajen bama mata jari, domin su dogara da kansu.To Alhamdulillah.

Me za ki ce da wannan shafi na Adon Gari?

Ba abunda zance wa adon gari Daya wuce fatan kara samun nasara da daukaka a fannin aikin su Allah ya kara musu farin jini a idanun Al-umma.

Me za ki ce da Jaridar Leadership Hausa?

Allah ya kara muku dunbum masoya ku yi suna sosai ta fannin aikin ku a idon duniya Ya sa ku zamo lamba na daya a duniya.

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Sosai kuwa abokan kuruciya da abokan zaman duniya na yau da kullum ina gaida iyalaina da ‘yan uwana fantan alkhairi ga abokan rayuwa ta na yau da gobe sun san kansu, ina gaida Bushira Aminu Nakura kawata Aminiyata Abokiyar shawarata

Na gode sosai.

Zagi
Bushira Nakura
+ postsBio
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Ba Ni Da Burin Da Wuce Ziyarar Kabarin Manzon Allah – Fauziyya Sani
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Ba Zan Taba Mantawa Da Zamowata Gwarzuwar Banki Sau Biyu A Jere Ba – Fatima Gana
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

MASU ALAKA

Mene Ne Ra’ayinku Kan Shigar Mata Harkokin Siyasa Gadan-gadan?
Taskira

Mene Ne Ra’ayinku Kan Shigar Mata Harkokin Siyasa Gadan-gadan?

September 5, 2026
Tsakanin Yanayin Sanyi Da Na Zafi Wanne Ya Fi Maka Dadi?
Taskira

Tsakanin Yanayin Sanyi Da Na Zafi Wanne Ya Fi Maka Dadi?

August 29, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?
Taskira

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Next Post
Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Zagi

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Zagi

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.