Kasar Sin ta bukaci kasa da kasa su sa ido kan duk wani yunkurin farfado da amfani da karfin soji daga Japan, tana cewa Tokyo ta riga ta kwaye lullubin da take fakewa da shi wajen kiran kanta “mai kaunar zaman lafiya.” Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Alhamis, lokacin da yake martani ga rahotannin da ke cewa gwamnatin Japan ta kare manufarta ta tsaro, bayan sanarwar hadin gwiwa da Sin da Pakistan suka fitar a karshen watan Mayu, wadda ta bayyana adawarsu da yunkurin sake farfado da amfani da karfin soji.
Rahotannin kafafen yada labarai sun ruwaito Japan na cewa, har yanzu ba ta sauya tafarkinta na kasa mai kaunar zaman lafiya wanda ke karkashin manufarta ta musammam mai mayar da hankali kan tsaro ba.
A cewar Lin Jian, Japan tana ci gaba da kara abun da take kashewa kan tsaro da sassauta ka’idojin kayyade fitar da makamai masu hadari, da kara jibge makamai masu linzami masu cin matsakaici da dogon zango, da fadada karfin soji na kai farmaki da tara kayayyakin makaman nukiliya masu yawa da kuma ingiza sake bitar kundin tsarinta na zaman lafiya.Ya kara da cewa, tuni Japan ta kwaye lullubinta na kasa mai kaunar zaman lafiya.
Don haka, ya kamata kasashen duniya su sa ido, kuma kada su bari ta sake dawo da amfani da karfin soji. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post