ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jawabin Shugaba Xi: Kasar Sin Ta Zama Baya-Goya-Marayu Ga Afirka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Shugaba

Masana da masharhanta da masu bin diddigin al’amuran da ke wakana a game da huldar kasar Sin da Afirka sun kasa kunne, sun zuba ido suna tsumayar abubuwan da taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC zai kunsa musamman a wannan karo da dandalin ke cika shekaru 24 da kafuwa.

Da yake ni dan Afirka ne, hankalina ya fi karkata a kan abin da zai fito daga bangaren kasar Sin, saboda yadda har yanzu muke fama da gibin kayayyakin more rayuwa da ci gaban tattalin arziki. Na bibiyi jawabin da Shugaba Xi Jinping ya gabatar na bude taron, inda na yi kicibis da abubuwa masu kara kwarin gwiwa game da kudurin kasar a kan Afirka, da yake nuna gaskiyarta wurin hulda da mu’amala da su har ta zama baya-goya-marayu a gare su.

  • “ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin
  • CHINADA Ta Nuna Shakku Ga Hukuncin Da Aka Yanke Kan Dan Wasan Tsalle-tsalle Da Guje-guje Na Amurka Game Da Shan Maganin Kara Kuzari

Abin da ya fi jan hankalina daga jawabin shi ne albishirin da Shugaba Xi ya yi wa Afirka na cewa kasarsa ta kimtsa tsaf domin aiwatar da wasu matakai na kawance guda 10 cikin shekaru uku kacal domin cimma burin zamanintar da kasashen. Sassan da za su ci gajiyar hakan sun hada da koyi da juna ta fannin wayewar kai, bunkasa kasuwanci, ci gaban masana’antu, hadewa da juna, hadin gwiwar samun ci gaban juna, kiwon lafiya, aikin gona da kyautata rayuwar jama’a, mu’amalar al’umma da musayar al’adu da kuma tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da al’amuran tsaro.

ADVERTISEMENT

Wadannan abubuwa ba kawai suna da muhimmanci ba ne ga ci gaban nahiyar Afirka, za su kuma taimaka wa kasashen yankin su kara fahimtar kawunansu don tsayawa da kafafunsu domin har yanzu akwai burbushin mulkin mallakar Turawan yamma cikin tsarin tafiyar da shugabanci da tattalin arzikinsu a fakaice.

Har ila yau, Shugaba Xi ya nuna yadda kasar Sin ke aiwatar da kawance da Afirka cikin ’yan uwantaka, yayin da a jawabin nasa ya yi kiran zurfafa ci gaban zamani mai adalci ga kowa ba shafaffu da mai ba kawai, da cin moriyar juna irin wanda zai fifita darajar dan Adam da amincewa da bambancin al’umma tare da tabbatar da tsaro da zaman lafiya. Abin burgewa, a wani yanki na jawabin shugaban, ya ce, “A kokarin da ake yi na zamanantarwa, bai kamata a bar wani ko wata kasa a baya ba.”

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Bugu da kari, jawabin ya nuna muhimmancin da Sin da Afirka suke da shi a duniya ta fuskar ci gaban zamani, kasancewar kashi daya bisa uku na daukacin mutanen duniya a kasar Sin da Afirka suke rayuwa, don haka ya ce ba za a samu nasarar zamanantar da duniya ba tare da zamanantar da Sin da Afirka ba.

Ina da yakinin cewa shugabanninmu na Afirka sun sake samun wani kwarin gwiwa na kyautatuwar al’amura da ci gaban kasashensu ba tare da hantara ba, a yayin da Shugaba Xi ya furta cewa, ya kamata a hade Sinawa da Afirkawa fiye da biliyan biyu da miliyan dari takwas a karkashin inuwa daya a matsayin wata kakkarfar runduna da za ta fuskanci samar da ci gaban zamani da ya dace da juna, inda hakan “zai rubuta sabon kyakkyawan babi na ci gaba a tarihin bil’adama”.

Irin wannan kawance ne nahiyar Afirka da ake wa kallon koma-baya ta fuskar ci gaba a duniya ta fi bukata, kuma kasar Sin ta nuna sahihancin kawancenta da yankin a zahiri bisa yadda aka samu ci gaba a fannonin sufuri, aikin gona, makamashi da sauran sassan da ta zuba jari na fiye da dala biliyan 200 a nahiyar. Duk da wadannan makudan kudade da ta zuba, da alama kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa Afirka ta fuskoki da dama, kamar yadda Shugaba Xi ya ce, Sin a shirye take ta tallafa wa Afirka wajen kara inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali cikin ’yanci ba tare da katsalandan ba, da fifita yankin a kokarin samar da zaman lumana a duniya.

Hakika jawabin Shugaba Xi ya nuna yadda kasar Sin ke son raya zumunci da ’yan uwantaka da Afirka wajen samar da kwararrun ma’aikata, da yaki da fatara da bunkasa samar da ayyukan yi da kyautata jin dadin rayuwar al’umma da inganta tsaro a zamanance ba tare da shiga-sharo-ba-shanu ba irin na kasashen yamma.

Shugaba
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
GORON JUMA’A 30-08-2024

GORON JUMA'A 6/9/2024

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.