Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce kafa wani karamin rukuni domin mayar da wani sashe saniyar ware, ba zai haifar da da mai ido ba, kuma hakan zai gurgunta yanayin amincewa juna, da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa.Â
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan a yau Litinin yayin da yake jagorantar taron manema labarai, lokacin da wani dan jarida ya tambaye shi game da tsokacin da shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi, game da tsarin dandalin hadakar kasashe hudu, wato Amurka, da Japan, da India da Australia, ya ce wannan hadaka ba komai ba ce illa wani makami da Amurka ke son amfani da shi wajen dakile kasar Sin, da kuma tabbatar da babakerenta.
- Ambaliya: Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Asusun Taimaka Wa Wadanda Annoba Ta Shafa
- Za A Gudanar Da Taron Tattaunawa Tsakanin Magadan Biranen Kasa Da Kasa
Jami’in ya ce har kullum Sin na yayata cewa, bai dace hadin gwiwa tsakanin kasashe ya zama makamin mayar da wani bangare saniyar ware ba, bare kuma illata moriyar wani bangare.
Game da amincewa da aka yi da yarjejeniyar cin gajiya daga fasahohin dijital na duniya bisa tsari, yayin taron kolin MDD kan makomar duniya, Lin Jian ya ce Sin na maraba da hakan. Kuma a mataki na gaba, Sin za ta yi aiki tare da sauran sassan kasa da kasa, wajen ingiza matakan aiwatar da yarjejeniyar, tare da hada hannu wajen gina al’ummar duniya ta dijital mai makomar bai daya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp