A yau 29 ga watan Yuni, kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jarida game da matakan kayyade fitar wa Japan kayayyaki.
Kakakin ya bayyana cewa, a ranar 24 ga watan Fabrairun 2026, bangaren Sin ya sanya kamfanoni 20 na Japan, ciki har da kamfanin kera jiragen ruwa na Mitsubishi a cikin jerin sunayen wadanda aka kayyade fitar musu kayayyaki, da kuma kamfanoni 20 na Japan, ciki har da kamfanin kera motoci na Subaru a cikin jerin wadanda ake sa ido kansu, da nufin dakile yunkurin Japan na “sake daukar makamai” da kuma neman mallakar makamin nukiliya. Ya bayyana cewa, abin takaici shi ne, a tsawon wani lokaci, bangaren Japan bai gyara kura-kurai ba, maimakon haka sai ya kara nisa a kan hanyar kuskure, tare da kara hanzarta “amfani da karfin soja”, da “sake daukar makamai”, da girke makaman kai hari, da kuma harba makamai a wajen kasar.
Don haka, bisa ga dokokin kasar Sin kamar “Dokar kayyade fitar da kayayyaki ta Jamhuriyar Jama’ar Sin” da “Dokar kayyade fitar da kayayyakin da ake iya amfani da su domin ayyukan farar hula da na soji ta Jamhuriyar Jama’ar Sin” da sauran ka’idoji, bangaren Sin ya yanke shawarar daukar matakai kamar haka: Na farko, sanya cibiyoyi 20 da suka shafi inganta karfin sojan Japan ciki har da cibiyar binciken tsaro a cikin jerin sunayen kayyadewa.Na biyu, sanya kamfanoni 20 na Japan ciki har da kamfanin kera na’urori na Mitsui E&S a cikin jerin sunayen da ake sa ido a kansu saboda rashin iya tantance wadanda za su yi amfani da kayayyakinsu domin ayyukan farar hula da na soji.
Wannan mataki na Sin an dauke shi bisa cikakken adalci da daidaito kuma ya dace da doka, wanda aka yi hakan don dakile yunkurin “sabon ra’ayin nuna karfin soja” na Japan. (Amina Xu)














