Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Rasha Maria Zakharova, ta ce kisan kiyashin Nanjing na kasar Sin da ya auku a ranar 13 ga watan Disamban 1937, ya yi sanadin daruruwan dubban rayukan fararen hula a birnin Nanjing, kuma alama ce karara ta zaluncin ra’ayin nuna karfin soja na Japan da laifukan da aka aikata wa bil adama.
Maria Zakharova ta nanata a jiya Alhamis cewa, babu shakku game da tarihin kisan kiyashin Nanjing. Tana cewa, kotun soji ta kasa da kasa ta gabas mai nisa, ta riga ta tabbatar da gaskiyar abun da ya faru ta hanyoyin shari’a, kuma tare da hukunce-hukuncen shari’o’in da aka yanke a Nuremberg na Jamus, sun hadu sun zama wani kwakkwaran tubalin odar duniya bayan yankin duniya na II da kuma tsarin da harkokin duniya ke gudana a yanzu. Ta ce duk wani yunkuri na kalubalantar wadannan hukunce-hukunce, farfadowa ne da ra’ayin kashe-kashe na Nazi ko na amfani da karfin soji ko kuma karyata laifuffukan da aka aikata, kuma dole ne kasa da kasa su yi tir da hakan da murya guda. (FMM)














