Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa na Kasa Dakta Abubakar Dantsoho ya nuna matukar jindadinsa, kan dawo da kasar nan, a cikin kungiyar kasa da kasa da ke kula da lafiyar da sufurin Jiragen Ruwa wato IMO.
Dantsoho ya bayyana cewa, dawo da kasar, ya nuna a zahiri cewar, Nijeriya ta kai makura a fadin duniya, wajen tafiyar da harkar sufurin Jiragen Ruwa a fadin duniya.
Idan za a iya tunawa, an zabo Nijeriya domin shiga cikin rukunun C ne, a ranar Juma’ar da ta gabata, a wani babban taro, da ya gudana a kasar Birtaniya.
- Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
- Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya
Shugaban ya bayyana cewa, wannan dawo da Nijeriya zuwa cikin kungiyar ta kasance tamkar abin tarihi a fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, musamman duba da cewa, Nijeriya ta shiga cikin matsayin na C a hukumance.
Dakta Dantsoho ya kara da cewa,”Kai wa wannan matsayin babban ci gaba ne, ga kasar nan, musamman ci gaban da aka samar na jagoranci na gari da bin ka’idojin gudanar da harkar sufurin Jiragen Ruwa na duniya da ake gudanarwa a kasar nan da jajircewarsu ministan bunkasa tattalin arzikin ruwa na teku Gboyega Oyetola, CON da kuma kokarin hukumomin da ke a karkashin ma’aikatar.
“Dawo Nijeriya a cikin rukunin na C a kungiyar ta IMO hakan ya nuna irin zagewar kasar nan na iya tafiyar da tsare-tsare da bin ka’idojin gudanar da sufurin Jiragen Ruwa da wanzar da tsaro da kuma samar da kyakyawan yanayi, ga fannin,” Inji Dantsoho.
“Wannan ci gaban, ba wai ga kasar nan ne kadai ba, har da ma ci gaban daukacin Afirka ta Yamma musamman a bangaren kara bunkasa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a nahiyar da samar da hanyoyin kara habaka safarar kaya zuwa ketare da kuma kara bunkasa fannin tattalin arziki na teku'” A cewar shugaban.
“Nijeriya a yau, ta kai wani babban mataki da duniya ke sauraronta a saboda haka, ina kara taya Nijeriya da hukumar ta NPA kan wannan nasarar da ta samu'” Inji Dantsoho.
Shugaban ya kuma yabawa ministan bunkasa tattalin arziki Dakta Adegboyega Oyetola, musamman kan jajircewarsa, wajen daga matsayin kasar nan, a fannin kula da lafiyar da sufurin Jiragen Ruwa na kasa
r nan.













