ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
Aliyu

A wannan mako da muke ciki ne, wakilinmu SANI ANWAR, ya zanta da Ɗan Majalisar Jihar Kano, mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, Injiniya Yusuf Bello Aliyu, wanda tattaunawar tasu ta ƙunshi batutuwa da dama, ciki har da batun zarge-zargen da suke yi wa gwamnan Jihar Kano, na cin amanar jagoransu na Kwankwasiyya da sauran wasu batutuwa da dama da suka shafi siyasar Kano da ma ƙasa baki-ɗaya. Ga dai yadda hirar ta kasance:

 

Ko za ka gabatarwa da masu karatu kanka?

ADVERTISEMENT

Sunana Hon. Injiniya Yusuf Bello Aliyu, ɗan majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, a zauren majalisa ta goma a Jihar Kano.

 

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani

Za mu so ka ɗan tsakuro mana kaɗan daga cikin gwagwarmayar siyasarka, sannan wane ne jagoranka na siyasa?

Alhamdu lillahi, muna gode wa Allah SWT, mai yin yadda ya so a lokacin da ya so. Tun muna jami’a muka fara gwagwarmayar siyasa, ba zan manta ba, muna jami’ar Wudil, na fara riƙe muƙamin ‘Social Director na Ciɓil Engineering’, daga bisani kuma na zama ‘Welfare Officer na Nigerian Uniɓersity of Engineering Student’, daga nan kuma na yi Sanata har sau biyu a ƙungiyar NAKSS (Kano State Sutudents Association), na kuma riƙe muƙamin ‘Speaker’ sau biyu a lokacin da ina aji huɗu a jami’ar.

 

A lokacin da ina aji huɗun dai a jami’a, akwai ƙungiya ta Kwankwasiyya a mazaɓata ta Gama da na tsunduma, muke kuma ba da gudunmawa a ƙungiyance. Bayan na kammala jami’a, sai na ɗora daga inda muka tsaya, wato wannan tsari na Kwankwasiyya da har gobe muke ciki.

 

A matsayina na Injina, a lokacin da nake aiki da kamfanonin gine-gine, akwai manya-manyan ayyuka da muka yi, lokacin da mai girma Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso yana gwamna. Mu ne muka gina jami’ar North West da sauran wasu manya-manya ayyuka, ina yin wannan aiki, ina kuma yin siyasa. Daga nan ne, sai na kafa wata ƙungiya na sa mata suna ‘MB Foundation’, a ƙarƙashin gidauniyar ne muke bai wa matasa aikin yi tare da bayar da tallafi, musamman ga waɗanda ba su da abin yi kwata-kwata.

 

Wannan dalili ne ya haska mana buƙatar shiga gwamnati, ta hanyar yin takara, duk da cewa; a lokacin ban ma san wace takara ya kamata na yi ba, kwamitin da muke zama da su a wannan ƙungiya ne suka ce lallai sai na yi takarar ɗan majalisar tarayya. Bayan nan ne, muka sake fitowa muka kafa wata ƙungiyar mai suna ‘Kwankwasiyya Youth Mobilization’, wadda har yanzu tana nan da ita muke yin aiki a ko’ina, tun daga matakin jiha, ƙaramar hukuma da kuma mazaɓa.

 

Bayan mun shiga jam’iyyar NNPP ne, Allah ya ba mu nasara, duk da ba mu samu takarar majalisar tarayya ba, sai muka samu ta majalisar jiha, inda muka samu nasarar cin zaɓe da ƙuri’u masu gagarumin rinjaye. Domin kuwa, a duk Kano, babu ɗan majalisar da ya samu yawan ƙuri’un da na samu da suka kai kimanin sama da 50,000, wanda yake biye min, ratata da shi ta ƙuri’a ta kai kimanin 25,000, shi yasa ko kutu ma bai kai ƙara ba, saboda zaɓe ne na kece raini.

 

Haka zalika, ba ni da wani jagora ko mudubi da muke kallo, tamkar Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, dukkannin nasarorin da muka samu, albarkacinsa muka ci, domin shi ne ya ba mu takara, ya yi gwagwarmayar tallata mu har muka samu gwamnati. Shi yasa na sha faɗa cewa, ko yanzu ya umarce ni da kada na fito takara, to wallahi zan haƙura ba zan fito ba.

Aliyu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Aliyu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Tattaunawa

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

April 4, 2026
Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani
Tattaunawa

Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani

March 28, 2026
2027: Dole Dattawan Arewa Su Hada Kai Domin Samar Wa Yankin Mafita —Alhaji Babangida Aliyu
Tattaunawa

2027: Dole Dattawan Arewa Su Hada Kai Domin Samar Wa Yankin Mafita —Alhaji Babangida Aliyu

February 6, 2026
Next Post
A Tattauna Da Boko Haram Don Sako Mana Mutane 416 Da Aka Kama – Ƙungiya A Borno

A Tattauna Da Boko Haram Don Sako Mana Mutane 416 Da Aka Kama - Ƙungiya A Borno

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.