A wannan mako da muke ciki ne, wakilinmu SANI ANWAR, ya zanta da Ɗan Majalisar Jihar Kano, mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, Injiniya Yusuf Bello Aliyu, wanda tattaunawar tasu ta ƙunshi batutuwa da dama, ciki har da batun zarge-zargen da suke yi wa gwamnan Jihar Kano, na cin amanar jagoransu na Kwankwasiyya da sauran wasu batutuwa da dama da suka shafi siyasar Kano da ma ƙasa baki-ɗaya. Ga dai yadda hirar ta kasance:
Ko za ka gabatarwa da masu karatu kanka?
Sunana Hon. Injiniya Yusuf Bello Aliyu, ɗan majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Nassarawa, a zauren majalisa ta goma a Jihar Kano.
Za mu so ka ɗan tsakuro mana kaɗan daga cikin gwagwarmayar siyasarka, sannan wane ne jagoranka na siyasa?
Alhamdu lillahi, muna gode wa Allah SWT, mai yin yadda ya so a lokacin da ya so. Tun muna jami’a muka fara gwagwarmayar siyasa, ba zan manta ba, muna jami’ar Wudil, na fara riƙe muƙamin ‘Social Director na Ciɓil Engineering’, daga bisani kuma na zama ‘Welfare Officer na Nigerian Uniɓersity of Engineering Student’, daga nan kuma na yi Sanata har sau biyu a ƙungiyar NAKSS (Kano State Sutudents Association), na kuma riƙe muƙamin ‘Speaker’ sau biyu a lokacin da ina aji huɗu a jami’ar.
A lokacin da ina aji huɗun dai a jami’a, akwai ƙungiya ta Kwankwasiyya a mazaɓata ta Gama da na tsunduma, muke kuma ba da gudunmawa a ƙungiyance. Bayan na kammala jami’a, sai na ɗora daga inda muka tsaya, wato wannan tsari na Kwankwasiyya da har gobe muke ciki.
A matsayina na Injina, a lokacin da nake aiki da kamfanonin gine-gine, akwai manya-manyan ayyuka da muka yi, lokacin da mai girma Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso yana gwamna. Mu ne muka gina jami’ar North West da sauran wasu manya-manya ayyuka, ina yin wannan aiki, ina kuma yin siyasa. Daga nan ne, sai na kafa wata ƙungiya na sa mata suna ‘MB Foundation’, a ƙarƙashin gidauniyar ne muke bai wa matasa aikin yi tare da bayar da tallafi, musamman ga waɗanda ba su da abin yi kwata-kwata.
Wannan dalili ne ya haska mana buƙatar shiga gwamnati, ta hanyar yin takara, duk da cewa; a lokacin ban ma san wace takara ya kamata na yi ba, kwamitin da muke zama da su a wannan ƙungiya ne suka ce lallai sai na yi takarar ɗan majalisar tarayya. Bayan nan ne, muka sake fitowa muka kafa wata ƙungiyar mai suna ‘Kwankwasiyya Youth Mobilization’, wadda har yanzu tana nan da ita muke yin aiki a ko’ina, tun daga matakin jiha, ƙaramar hukuma da kuma mazaɓa.
Bayan mun shiga jam’iyyar NNPP ne, Allah ya ba mu nasara, duk da ba mu samu takarar majalisar tarayya ba, sai muka samu ta majalisar jiha, inda muka samu nasarar cin zaɓe da ƙuri’u masu gagarumin rinjaye. Domin kuwa, a duk Kano, babu ɗan majalisar da ya samu yawan ƙuri’un da na samu da suka kai kimanin sama da 50,000, wanda yake biye min, ratata da shi ta ƙuri’a ta kai kimanin 25,000, shi yasa ko kutu ma bai kai ƙara ba, saboda zaɓe ne na kece raini.
Haka zalika, ba ni da wani jagora ko mudubi da muke kallo, tamkar Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, dukkannin nasarorin da muka samu, albarkacinsa muka ci, domin shi ne ya ba mu takara, ya yi gwagwarmayar tallata mu har muka samu gwamnati. Shi yasa na sha faɗa cewa, ko yanzu ya umarce ni da kada na fito takara, to wallahi zan haƙura ba zan fito ba.















Discussion about this post