Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da shirin horar da matasa akalla 50,000 a fadin jihar a shekarar 2026 a matsayin wani bangare na kokarin dakile rashin aikin yi da kuma bunkasa dogaro da kai a fannin tattalin arziki.
Gwamna Abba Yusuf ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi yayin raba kayan aiki ga wadanda aka kammala horaswa 2,260 daga cibiyoyin koyon sana’o’i takwas a gidan Gwamnati, Kano.
- Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Bunkasa Sayayya Da Bude Kofa A Shekarar 2026
- Gwamnatin Katsina Ta Bayyana Dalilin Sakin Mutane 70 Da Ake Zargi Da Ta’addanci
A cewar wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Dawakin Tofa ya fitar a ranar Lahadi, shirin yana da nufin samar wa matasa dabarun aiki don ba su damar zama masu bayar da gudummawa ga tattalin arzikin jihar.
Da yake jawabi a wurin taron, Yusuf ya ce an tsara shirin ne don gina matasa masu kwarewa da dogaro da kansu wadanda za su iya samar da ci gaba mai dorewa.
“Manufarmu ita ce karfafa wa matasa gwiwa da kwarewa da damar da suke bukata don tsayawa da kansu, samun abin rayuwa da kuma bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban jihar Kano,” in ji gwamnan.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post