ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Ta Bayyana Dalilin Sakin Mutane 70 Da Ake Zargi Da Ta’addanci

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta kare matakin da ta ɗauka na amincewa da sakin mutane 70 da ake zargi da hannu a laifukan ta’addanci, inda ta bayyana hakan a matsayin dabarar ƙarfafa zaman lafiya a yankunan da ke fama da matsalar tsaro.

Kwamishinan Harkokin Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Mu’azu, ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da DCL Hausa, yana mai cewa sakin mutanen na daga cikin matakan gina amana da aka cimma tsakanin ƙananan hukumomin da abin ya shafa da kuma ƴan bindiga da suka tuba.

  • Gwamnatin Katsina Ta Sanya Motocin Daukar Marasa Lafiya 15 A Manyan Hanyoyi
  • Mutum Biyu Sun Rasu Yayin Rikici Tsakanin Jami’an Tsaro Da Matasa A Katsina

A cewar Mu’azu, yarjejeniyar zaman lafiyar da ta shafi aƙalla ƙananan hukumomi 15 ta haifar da sakamako mai kyau, ciki har da sakin kusan mutane 1,000 da aka sace a hare-haren ƴan bindiga a baya. Ya kwatanta matakin sakin waɗanda ake zargi da musayar fursunoni a lokacin yaƙe-yaƙe, wadda ake yi domin ƙarfafa zaman lafiya da hana sake ɓarkewar rikici.

ADVERTISEMENT

Bayyanar ta biyo bayan martanin jama’a kan wata takardar sirri da ta bayyana cewa Ma’aikatar Shari’a ta jihar ta ɗauki matakan doka domin ganin an saki mutanen, da dama daga cikinsu na fuskantar shari’a.

Takardar, wadda Sahara Reporters ta fara wallafa wa, an rubuta ta ne a ranar 2 ga Janairu, 2026, kuma ta nemi sa hannun Kwamitin Kula da Aiwatar da Dokar Shari’ar Laifuka (ACJMC) domin sauƙaƙa sakin waɗanda ake tsare da su bisa sharuɗɗan yarjejeniyar zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Kwamishinan ya ƙara da cewa yarjejeniyar ta haifar da sakin mutane a ƙananan hukumomi da dama kamar Sabuwa, da Bakori, da. Danmusa, da Dutsinma, da Kurfi, da Safana, da Malumfashi da kuma Jibia, inda wasu wurare suka samu sakin ɗaruruwan mutane.

Ya jaddada cewa wannan mataki bai saɓa wa doka ba, yana mai cewa duk wanda bai gamsu da matakin ba na da ƴancin bin hanyoyin shari’a. Duk da haka, lamarin na ci gaba da jawo muhawara, inda wasu ke ganin hakan na iya raunana adalci, yayin da wasu ke cewa zaman lafiya mai ɗorewa na buƙatar tattaunawa da sassauci.

Katsina
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Za Ta Horar Da Matasa 50,000 A Shirin Koyon Sana'o'i

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.